Saturday, June 27
Shadow

Gwamnan jihar Rivers da Tinubu ya dakatar, Fubara ya je gidan Wike dan neman a sasanta, ji yanda ya kwanta kasa yana rokon Wike

Rahotanni sun bayyana cewa, dakataccen gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara ya je gidan ministan Abuja, Nyesome Wike dan neman a sasanta.

Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da Fubara ya gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a birnin Landan.

Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun da tsohon gwamnan jihar, Olusegun Osoba ne suka yiwa Fubara jagoranci zuwa gidan Wike.

Rahoton yace Fubara ya kwanta kasa ya gaishe da Wike inda ya rika kiransa da Ogana Ogana. Wata majiya tace sai can duhu yayi sosai sannan Fubara ya bar gidan.

Hakanan majiyar ta kara da cewa, Wike ya bukaci Fubara ya je ya tara mutanensa ya gaya musu ainahin abinda ya hadasu fada.

Karanta Wannan  Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Kakakin Wike, Lere Olayinka ya tabbatar da faruwar lamarin amma bai bayar da cikakken bayanin abinda ya faru ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *