Saturday, June 27
Shadow

Kotu ta ki amincewa da bukatar Gwamnatin tarayya ta kama Sanata Natasha Akpoti

Kotun tarayya dake Abuja ta ki amincewa da bukatar Gwamnatin tarayya ta kama dakatacciyar sanata Natasha Akpoti.

Gwamnatin na son a kama Sanata Natasha Akpoti ne saboda kun ta ki bayyana a kotu wajan shari’ar da ake yi ta zarginta da bata suna.

Mai shari’a, Justice Muhammed Umar ne ya yanke wannan hukunci bayan da lauyan gwamnatin tarayya, David Kaswe, ya nemi a kama Sanata Natasha Akpoti saboda kin halartar kotun duk da cewa an baiwa Lauyanta Sammace.

Saidai Mai Shari’a Muhammad Umar ya bayyana cewa, tunda ba Sanata Natasha Akpoti da kanta aka baiwa samacen ba ba za’a iya cewa lallai ta samu sammacen ba.

Karanta Wannan  Hedikwatar Tsaro Ta Kasa Ta Yi Wa Babban Soja MS Adamu Gayyatar Gaggawa Domin Ya Zo Ya Yi Bayanin Dalilinsa Na Azabtar Da Soja Abbas Har Na Tsawon Shekaru Shida

Dan haka ya daga ci gaba da sauraren shari’ar zuwa ranar 30 ga watan Yuni.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *