Friday, December 5
Shadow

Da Duminsa: Wike ya gayawa shugaba Tinubu wata maganar da bata kamata ba kuma maganar ta fito, ji abinda yace

Rahotanni sun ce ministan Abuja Nyesom Wike ya fadi abinda bai kamata ba akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Ana ganin Wike a matsayin na hannun damar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu wanda ke abinda ya ga dama a gwamnatin Tinubu ba tare da an taka masa burki ba.

A kwanannan aka ruwaito cewa Wike ya baiwa ‘ya’yansa biyu filaye masu yawa a Abuja.

Hakanan kuma ya baiwa iyayensa da ‘yan uwa filayen.

A wani sabon labari da jaridar Peoplesgazette ta ruwaito, tace Wike yace babu abinda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai masa.

Sannan babu wani alkalin da ya isa ya daureshi a Najeriya.

Hakan na zuwane bayan da ake kira ga shugabab kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauki mataki akan yanda Wike ke abinda ya ga dama a Gwamnatinsa.

Karanta Wannan  Karanta Abubuwa 13 game da Kudirin Harajin da Shugaba Tinubu ya nace sai ya aiwatar duk da Kwamitinsa na tattalin arziki shun bashi shawarar kada ya aiwatar da kudirin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *