Friday, December 5
Shadow

Tinubu ya faɗa wa ‘yanmatan Najeriya ‘ku ciyo mana kofi’

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya nemi tawagar ƙwallon ƙafa ta matan ƙasar da ta kai masa kofin gasar ƙasashen Afirka yayin da suke shirin buga wasan ƙarshe a yau Asabar.

Najeriya za ta kara da mai msaukin baƙi Morocco a birnin Rabat domin neman lashe kofin a karo na 10 jimilla, yayin da Moroccon ke neman kofin a karon farko.

“A madadin ƙasar nan baki ɗaya, muna goyon bayanku tare da yin addu’ar ku yi nasara a daren yau, yayin da kuke neman kafa tarihin cin kofi na 10,” a cewar Tinubu cikin sanarwar da fadar shugaban ta fitar.

Karanta Wannan  Da gangan wasu mugayen 'yan Najeriya ke kara farashin kaya dan kawai su bata min suna>>Gwamnatin Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *