Friday, December 5
Shadow

Mayar da takarar Shugaban kasa na PDP zuwa kudu, kokari ne na taimakon Tinubu ya ci zabe>>Inji Gbenga Olawepo-Hashim

Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Gbenga Olawepo-Hashim ya zargi jam’iyyar PDP din da yunkurin taimakin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sake cin zabe.

Ya bayyana hakane bayan da jam’iyyar PDP tace dan kudu zata tsayar takarar shugaban kasa inda Gbenga yace hakan yunkuri ne na taimakawa Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ci zabe a 2027.

Ya bayyana hakane a yayin hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace masu neman a tsayar da dan kudu takarar shugaban kasar irin wanda suka raba kafa ne a PDP suna cewa, suna tare da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu amma kuma suna cikin PDP.

Karanta Wannan  SERAP ta ɓuƙaci Tinubu ya hana ministan Abuja da gwamnoni bai wa alƙalai motoci da gidaje

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *