Friday, February 13
Shadow

Tun da na hau mulki cin hanci ya zama tarihi a Nijeriya – Tinubu

Tun da na hau mulki cin hanci ya zama tarihi a Nijeriya – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar wa masu saka hannun jari na kasar Brazil cewa gyare-gyaren tattalin arzikin da ake aiwatarwa a Najeriya suna samar da ingantattun sakamako, inda ya yi ikirarin cewa “ba a sake samun cin hanci da rashawa ba” tun bayan da ya hau kujerar shugaban kasa.

Jaridar Tribune ta rawaito cewa Shugaban ya bayyana hakan ne a yayin wani taro da aka gudanar a ranar Litinin tare da ministoci daga kasashen biyu da kuma mambobin kungiyar kasuwanci ta Brazil, inda ya sake jaddada shirye-shiryen Najeriya na karfafa hadin gwiwa a bangaren fasahar zamani, samar da abinci, masana’antu da makamashi.

Karanta Wannan  Rikicin jam'iyyar APC ya kara kazancewa, Sakataren jam'iyyar ya mayarwa Wike da martani

Tinubu ya bayyana tattalin arzikin Najeriya a matsayin “wata babbar kasuwa mai dimbin damammaki da kamfanonin Brazil ba su taba cin moriyarta ba.”

Ya amince cewa gyare-gyaren da ya fara aiwatarwa “sun kasance masu zafi a farko, amma a yau sakamakon yana bayyana.”

“A hankali jama’a suna fahimta. Muna da karin kudade a cikin tattalin arziki, kuma babu cin hanci da rashawa.”

Don nuna gaskiya da adalci, ya yi nuni da Babban Bankin Najeriya (CBN), inda ya ce: “Ba sai ka san wani ba kafin ka samu kudin waje da kake bukata. ‘Yan wasa da karairayi sun fita daga kasuwa. A kasuwar kudin mu, kofa a bude take ga dukkan kasuwanni.”

Karanta Wannan  Hotunan Yadda Iyalan Tsohon Gwamnan Jihar Ondo, Marigayi Arakunrin Oluwarotimi Akeredolu, Suka Kawata Kabarinsa A Mahaifarsa, Owo Na Jihar Ondo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *