Friday, December 5
Shadow

Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana’a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, tana nan akan bakanta na cewa, kowa sai ya biya haraji.

Shugaban kwamitin Gyaran fasalin kudi na shugaban kasa, Taiwo Oyedele ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labarai.

Yace a Duniya gaba daya haka tsarin yake, ko ta wace hanya ka samu kudi sai ka biya Haraji, yace idan ance wanda suka samu kudi ta hanyar Halal ne kadai zasu biya haraji, to sai wasu su koma samun kudi ta hanyar Haram dan su kaucewa biyan Harajin.

Yace hukumar karbar Haraji ta kasar Amurka nada taken cewa ko sata kayi sai ka biya Haraji.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Matashi ya bayyana cewa, a shirye yake ya auri Ummi Nuhu idan ta amince

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *