Friday, December 5
Shadow

Bayan da mahaifin Bilyaminu ya fito ya ce ya yafewa Maryam Sanda kuma shine ma yayi kokarin ganin Shugaba Tinubu ya yafe mata, Wani dan Uwan Biliyaminun ya fito yace bayan rasuwar Biliyaminu, Mahaifin ya hanasu sakat akan Gado, Aka bashi Miliyan 5 amma yace bai yadda ba, ya je kotu saida aka bashi Miliyan 10 daga cikin kudin gadon

Bayan Fitowar mahaifin Bilyaminu, watau mijin Maryam Sanda wanda ta kashe yace ya yafewa Maryam Sanda, Asalima Shine ya shiga gaba wajan ganin shugaba Tinubu ya yafewa Maryam din.

Wani dan uwan mamacin ya fito yace Malam Bello Halliru da aka kashe Bilyaminu ya rika damunsu kan maganar gado aka bashi Naira Miliyan 5, amma bai yadda ba, sai da ya kai kotu aka kara masa zuwa Naira Miliyan 10.

Yace amma shine zai fito yana wannan magana.

Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta.

Yafewa Maryam Sanda da shugaba Tinubu yayi ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke ganin hakan bai kamata ba.

Karanta Wannan  Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Kalli Bidiyon Da Duminsa: Mummunan Abinda Tshagyeran dhajiy sukawa Sojowjin da aka aika su kubutar da dalibai 'yan mata 'yan makarantar jihar Kebbi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *