Wednesday, September 2
Shadow

Dalibai Kiristoci na Jami’o’in Federal University Kashere, Gombe da BUK Kano sun koka da cewa akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya

Daliban jami’o’in Federal University Kashere, Gombe dana jami’ar BUK, Kano Kiristoci sun koka da cewa, akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya.

Daya daga cikin daliban na Kashere ne ya fito yake zanga-zanga shi kadai inda yace suna bukatar Coci a jami’ar.

Wani kirista ta bayyana cewa abin haushin shine jihar Gombe da yawan musulmai da kirista daidai suke watau 50/50 amma irin wannan abin na faruwa.

Karanta Wannan  Tanko Yakasai yayi kiran Arewa ta ci gaba da goyon bayan Shugaba Tinubu saboda kokarinsa na tada komadar tattalin arziki na samar da sakamako me kyau

Wannan zanga-zanga da dalibin yayi tasa shima wani dalibin jami’ar BUK Kano ya bayyana cewa suna hakan take, akwai masallatai a BUK amma su ba’a basu damar gina coci ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *