Thursday, December 11
Shadow

Tura sojoji kasar Benin Republic da shugaba Tinubu yayi babban laifine da ya kamata ace an tsigeshi daga shugabancin Najeriya>>Inji Lauya

!Babban lauya me suna Marshal Abubakar ya bayyana cewa aika sojojin Najeriya zuwa kasar Benin Republic da shugaba Tinubu yayi babban laifine da ya kamata ace an tsigeshi daga mulki.

Yace tura sojoji zuwa wata kasa doka ta tanadi cewa sai majalisa ta amince amma shugaba Tinubu yayi gaban kansa.

A jiya shugaba yi ya aika da sojojin sama dana kasa dan su dakile yunkurin juyin mulkin kasar ta Benin Republic

Saidai Lauyan yace wannan mataki ya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Karanta Wannan  Ka Mayarwa Da PDP Da Sauran Ma'aikatun Da Ka Karbe Musu Ofisoshinsu, Amma Ka Tabbatar Sun Biya Harajin Nan Da Makonni Biyu, Umarnin Tinubu Ga Ministan Abuja, Wike

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *