
Sanata Ali Ndume daga jihar Borno yace shi da iyayensa duk musulunta suka yi.
Yace ya taso a matsayin Kirista kuma ya je makarantar Kiristoci.
Sannan yace a da sunansa Samuel amma aka ce ya je ya shiga Musulunci ya koma Mohammed, sannan yace mahaifiyarsa ma tana cikin matan zumunta amma daga baya duk sun musulunta.
Saidai yace a gidansu raba kafa aka yi, wasu suka zama musulmai, was suka zama Kirista ta yanda duk inda ta fadi sha.