
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata gina titin jirgin kasa na cikin gari da zai rika jigilar mutane a jihar Kano.
Hakan ya fitone daga bakin gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.
Yace Gwamnatin zata kashe Naira Tiriliyan 1 wajan gina wannan titin jirgin.
Ya bayyana cewa wannan na daga dalilan da suka sa ya koma jam’iyyar APC dan hada kai da Gwamnatin tarayya wajan kawowa jihar Kano ci gaba.