
Rahotanni daga majalisar Dattijai sun bayyana cewa, sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi ta shiga ofishin sanata Titus Zam inda take ta babatu akan cewa an cire sunanta daga kwamitin da zasu kula da kasafin kudin hukumar ci gaban Arewa ta tsakiya.
Sanata Natasha Akpoti ta rika fadin cewa, ba zata amince da wannan abu ba inda aka ana rike wani dake kokarin kai Naushi.
Sanata Natasha Akpoti dai tace wannan daya ne daga cikin kokarin da ake na tauyewa mutanen mazabarta hakkinsu, tace babu wani sanatan da yafi wani, duk daya suke.