Wednesday, March 4
Shadow

Masu zagin Janar TY Danjuma cewa bai son Musulmi dana fito takarar gwamna a jihar Zamfara ya bani kyautar dala $500,000 saboda idan na ci zabe in magance matsalar tsaro>>Sanata Dansadau

Sanata Saidu Muhammad Dansadau ya bayyana cewa, ba gaskiya bane zagin da akewa Janar TY Danjuma cewa bai son Musulmi.

Ya bayyana hakane a wajan wa’azin da yake a masallacin Apo Legislative Quarters.

Yace da yake sun yi Sanata tare da matar TY. Danjuma, ta rika bashi labarin cewa da zai samu gwamnan Zamfara da an magance matsalar tsaro.

Yace da ya fito takara sai matar TY Danjuma ta gaya masa cewa ga wanda yake bashi labari.

Yace Janar TY Danjuma ya aika masa Tallafin dala $500,000.

Karanta Wannan  Matashiya 'Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *