Tuesday, March 24
Shadow

Kwankwaso zai koma jam’iyyar ADC ranar Laraba

Rahotanni sun bayyana cewa, Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso zai koma jam’iyyar ADC nan da ranar Laraba.

Rahoton yace Kwankwaso zai koma jam’iyyar ADC ne a garinsa inda ake tsammanin zai yanki katin jam’iyyar acan.

Rahoton wanda ya fito daga the Whistler yace a kwanakinnan, Kwankwaso ya gana da wasu jiga-jigan jam’iyyar na ADC wanda hakan yasa ake kara kyautata zaton komawarsa jam’iyyar.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Likafa ta yi gaba inda aka ga Iftihal Madaki a karo na biyu tana rawa da Soja Boy

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *