
A yau, Laraba, Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban babbar kotun tarayya dake Kaduna inda kotun zata saurari bukatarsa ta neman beli.
Wani abu da ya dauki hankula shine ganin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da hatimin jam’iyyar ADC a jikin rigarsa.
An baza jami’an tsaro a farfajiyar Kotun inda aka hana zirga-zirga a wajan.
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhumen aikata ba daidai ba a ofishinsa da kuma almundahanar kudade.