Saturday, June 27
Shadow

Da Duminsa:Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a kotu a yau sanye da tutar jam’iyyar ADC

A yau, Laraba, Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban babbar kotun tarayya dake Kaduna inda kotun zata saurari bukatarsa ta neman beli.

Wani abu da ya dauki hankula shine ganin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da hatimin jam’iyyar ADC a jikin rigarsa.

An baza jami’an tsaro a farfajiyar Kotun inda aka hana zirga-zirga a wajan.

Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhumen aikata ba daidai ba a ofishinsa da kuma almundahanar kudade.

Karanta Wannan  Jam'iyyar PDP ta lashe gaba dayan zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Osun

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *