
Hukumar sojojin Najeriya ta baiwa ‘yan Najeriya hakuri saboda rashin ganin canji a harkar tsaro duk da zuwan sojojin Amirka.
Me magana yawun hukumar Major General Micheal Onoja ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai.
Yace sojojin na Amirka suna aikin bayar da bayanan sirri ne amma basa yaki.
Yace ‘yan Najeriya su yi hakuri sai a hankali za’a fara ganin Chanji.