Friday, April 3
Shadow

Gwamnoni, Dangote da sauran ‘yan kasuwa sun tarawa matar shugaban kasa, Remi Tinubu Naira Biliyan 66 a rana daya bayan kaddamar da gidauniyar neman Tallafi

Bayan kaddamar da gidauniyar neman tallafin ciyar da talakawa da matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta yi a ranar Alhamis.

Gwamnoni da Dangote da sauran ‘yan kasuwa sun tara mata Naira Biliyan 66.

Ministan lafiya da walwala, Prof Ali Pate ne ya tabbatar da hakan a jawabin da yayi.

Rahoton yace Dangote ya bayar da tallafin Naira Biliyan 20.

Kamfanin mai na kasa, NNPCL sun bayar da tallafin Naira Biliyan 10

Wasu abokan matar shugaban kasar sun bayar da tallafin Naira $500,000. Gidauniyar The Emeka Offor Foundation ta bayar da tallafin Naira Miliyan 500.

Yace hakanan shugaba Tinubu ya amince a fitar da Naira Biliyan 17 dan wannan aiki.

Karanta Wannan  Zulum zai mayar da 'yan gudun hijira 6,000 gidajensu saboda 'ƙaruwar karuwanci' a sansanoni

Sannan kowace jihar Najeriya ana tsammanin ta bayar da tallafin Naira Miliyan 500 wanda idan jihohi 36 suka bayar, Za’a tashi da Naira Biliyan 18 kenan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *