
Rahotanni sun bayyana cewa yayin da ake fama da Nafiu Bala Gombe, wani tsagi na jam’iyyar ADC ya bayyana inda suke ikirarin cewa, sune shuwagabannin jam’iyyar na gaskiya.
Tsagin wanda wani me suna Don Norman Obinna kejagoranta, sun bayyana hakane a ganawa da manema labarai da suka yi a Abuja ranar Talata.
Sun ce tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu da ya mikawa su David Mark ragamar jam’iyyar, tun shekarar 2022 wa’adin mulkinsa ya kare, kuma dama akwai shari’a da ake yi dashi a kotu bama guda daya ba.