
Wani na kusa da Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, El-Rufai zai tsaya takarar shugaban kasa.
Rahotan ya watsu sosai a kafafen sada zumunta.
Saidai a martaninsa ta bakin me magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, wannan Rahotan ba gaskiya bane.
Yace wani ne na kusa dashi ya bayyana ra’ayinsa amma ba daga bakinsa maganar ta fito ba.
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya ce ba zai ji tsoron fitowa ya bayyana ra’ayinsa na siyasa ba idan yanaso.