
Mutanen jihar Kwara sun ki karbar tallafin da aka kai musu na gwamnatin tarayya, karkashin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
A wani Bidiyo da ya rika yawo a kafafen sada zumunta, an ga mutanen na jihar Kwara na cewa basa son tallafin kowa yaki karba.
Jihar Kwara dai na daga cikin jihohin dake fama da matsalar tsaro sosai.
A baya ma, Jihar Benue sun fito sun ce basa son tallafin shinkafa na Gwamnatin Tinubu inda suka ce ba shine matsalarsu ba.