
Tauraron fina-finan Hausa, Muhammad S. Bashir ya bayyana cewa, Tijjaniyya daban Addinin Musulunci daban.
Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa da ya watsu a kafafen sada zumunta inda aka ganshi yana sukar ‘yar Tijjaniyya da cewa, An gayawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) kalaman da basu dace ba amma basu fito sun kare ba.
Yace amma da jawahilin ma’ani da shehunansu aka taba da yanzu kaji su suna cewa an keta janabin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam).