
Tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa, ya gano wani shirin Makarkashiya da ake shirya masa a game da takarar Gwamnan jihar Gombe da ya fito.
Ya bayyana cewa, Wasu ne suka yi riguna da fastarsa a jikin rigunan suka saka dan kawo hargitsi a wajan zaben fidda gwani da ake yi a jihar.
Yayi kira ga masoyansa da kada su saka irin wannan riga.
Yace kuma yana kira ga jami’an tsaro da su dauki mataki akan irin wadannan mutanen.