
‘Yan majalisa da yawa ne suka ki amincewa da bukatar abokin aikinsu Yusuf Gadgi bayan da yayi kiran cewa ya kamata su gayyaci shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya musu bayani kan matsalar tsaro.
A Bidiyon da yake ta yawo a kafafen sada zumunta, An ga Yusuf Gadgi a mike yana jawabin cewa a gayyaci shugaba Tinubu.
Saidai an ji da yawa ‘yan majalisar na masa ihun cewa basu amince ba ya zauna.
Hakan ya baiwa ‘yan Najeriya da yawa mamaki inda wasu ke tambayar shin ‘yan majalisar wa suke wakilta kuma zaman me suke a majalisar?