
Sheikh Salihu Zaria ya mayarwa da Dr. Jamil Dutsen Tanshi Martani bayan da ya gaya masa cewa, bai kamata ziyarar da ya kaiwa Dr. Junaidu ba.
An ga Shaikh Salihu Zaria ya kaiwa Dr. Junaid ziyara har masallacin da yake karatu inda shima yayi fadakarwa.
Saidai Dr. Jamilu yace wannan ziyara bata dace ba dan ga Ahlussunah nan da yawa a Bauchi, Malam bai kai musu ziyara ba sai Dr. Junaid.
A martaninsa, Sheikh Salihu Zaria yace ya gode da kiran ya ji tsoron Allah da Dr. Jamilu ya masa yace amma ya rika shan ruwan alwala ko zuciyarsa ta yi sanyi.
Yace kuma shi baya boye akidarsa ko ina yaje shi Dan Izala ne sannan kuma Najeriya ce ta hadasu.