
Tauraron fina-finan Hausa, Saheer Abdul ya saiwa matarsa Mota da wayar iPhone 17 sannan ya biya mata Makkah.
Ya bayyana a cikin wani Bidiyo yana cewa matar tasa a lokacin da zai aureta an rika zugata ana cewa karta auri me bi gida-gida yana tallah.
Yace kuma akwai masu kudi dake neman aurenta amma taki binsu ta bishi.
Yace saboda wannan halacci da ta masa yasa yake son saka mata da Alheri.