
A yaune dai Rahotanni suka watsu cewa, Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya saki matarsa Maimuna shekara daya bayan aurenta.
Hakan ya zowa mutane da mamaki musamman ganin cewa dama a baya ana zargin Adam A. Zango da auri saki.
Maimuna dai ta fito ta tabbatar da cewa, Adam A. Zango ya saketa inda tace kadararta kenan.
A yanzu kuma kafar AGG Media ta wallafa wata Hira da ta yi da Adam A. Zango amma bai yi magana akan maganar sakin auren nasa ba.