
Ana zargin Daya daga cikin manyan yaran dan takarar Gwamnan jihar Gombe, Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami, watau Abba Pantami da yin wallafa a shafinsa na sada zumunta inda ya rubuta cewa, Idan Pantami ya ci zaben gwamnan jihar Gombe zai hana Maulidi.
Screenshot na rubutun nasa yana ta yawo a kafafen sada zumunta inda ake ta sharhi akai.
Inda a shafin Tauraron fina-finan Hausa Baba Sadiq aka fara ganin screenshot din wanda daga baya ya ci gaba da yaduwa.
Zuwa yanzu dai Abba Pantami bai ce komai kan lamarin ba.

