Wednesday, August 26
Shadow

Dole sai mun dauki matakai na shan wahala kamin a samu gyara a kasarnan>>Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu

Gwamnatin tarayya ta bakin Ministan ci gaban yankunan kasarnan, Abubakar Momo ta bayyana cewa dolene sai Gwamnatin ta dauki matakan shan wahala kamin a samu warware matsalolin kasarnan.

Ministan yace Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana nufin Najeriya da Alherine.

Ya bayyana hakane a Akure wajan kaddamar da rabon kayan tallafi ga jihohin Yankin Naija Delta.

Ministan yace kwanannan za’a ga amfanin gyare-gyaren da gwammatin Tinubun ke kawowa.

Yace idan dai ana son kawo gyara sai an dauki matakan shan wahala tukuna.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon Da Duminsa:Yanda Matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta kùnyàtà gwamnan jihar Osun yayin da yake tsaka da jawabi tace ta bashi minti 5 ya gama jawabin da yake ya wuce ya ishesu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *