
Jaruma Hassana Muhammad wacce aka fi sani da Safiya a shirin Zabi Biyu ta sanar yanzu cewa ta bar film saboda jin maganar mahaifiyarta, amma za ku gan ta a Zabi biyu zango na biyu da kuma uku tunda ta sanya hannu a yarjejeniyar shirin kuma an gama aikin zango na biyu an kusa gama na uku.
Sai kuma watakila wasu daidaikun shirye-shiryen da ta yi wanda bayan su ba za a sake ganin ta ba.
Wane fata zaku yi mata?
Daga Mutawakkil Gambo Doko