Tuesday, February 3
Shadow

An baiwa mataimakin Gwamnan Kano umarnin sauka daga mukaminsa

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya ya baiwa mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo Umarnin sauka daga mukaminsa.

Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi inda yace Gwamna da mataimakinsa na tafiya a tikiti daya ne dan haka mataimakin Gwamnan idan ba zai iya bin Abba ba, abu mafi kyawu da zaiyi shine ya sauka daga mukaminsa.

Ya kara da cewa tunda dai yaga ba zai iyawa jagoransa biyayya ba kawai ya sauka daga mukamin.

Karanta Wannan  Magoya bayan Arsenal kenan a Kaduna ke yin liyafar murnar doke Real Madrid a gasar zakarun Turai a jiya da daddare

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *