Thursday, February 12
Shadow

An bayyana sunayen wadanda suka zuga kasar Amurka ta hana Kwankwaso Visar shiga kasarta sannan ta kwace kadarorinsa

A jiyane ne dai kasar Amurka ta fara shirin daukar mataki kan hana wasu ‘yan Najeriya Visa ta shiga kasarta da kuma keace kadarorinsu saboda zargin suna cikin masu dakile ‘yancin yin addini.

Daga cikin wadanda kasar ta Amurka zata dauki mataki akansu akwai tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.

Da yake magana a wata hira da aka yi dashi.

Na kusa da Kwankwaso, Injiniya Buba Galadima ya bayyana cewa, gidan talabijin na Arise TV, da gidan jaridar Thisday da wasu ‘yan siyasa ne suka zuga kasar Amurka akan Kwankwaso.

Yace ko maganar shari’a da aka yi a Arewa, Kwankwaso bai yi shari’ar Musulunci a Kano ba.

Karanta Wannan  Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *