
Fasto Elijah Ayodele wanda ya saba kawo maganganu masu jawo cece-kuce yace nan da shekarar 2027 wani shugaban kasa zai garzaya Barzahu.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar, saidai bai yi karin haske game a sanarwar ba domin bai fadi sunan shugaban kasar ba.
A baya dai ya yi ta fadar irin wadannan abubuwan na hasashe inda yakan ce an masa wahayi.