
Wasu musamman ‘yan Arewa na sukar tsohon hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad da shishigi da neman mukami a Gwamnatin Tinubu.
Malam Bashir Ahmad dai yakan rika yada manufofin gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dana jam’iyyar APC.
Saidai da alama lamarin bayawa wasu ‘yan Arewa dadi inda wasu ke zarginsa da shishigi, wasu kuwa sun ce mukami yake nema.