Saturday, December 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

DJ ya dakatar da kida bayan da aka hanashi Abinci a wajan taro

DJ ya dakatar da kida bayan da aka hanashi Abinci a wajan taro

Duk Labarai
Wani DJ me saka kida, ya dakatar da kida a wajan bikin da ya je bayan da aka hanashi abinci yayin da ake ta baiwa sauran mutanen abinci. DJ din ya dakatar da kidan sannan ya kashe Janareta dan ya nuna fushinsa. A wani Bidiyonsa da ya watsu a kafafen sada zumunta, an ga DJ din yana kumfar baki da fadin cewa, ba'a masa adalci ba. Saidai daga baya an bashi baki inda aka masa alkawarin samar masa da abinci da zai ci.
Maza sun yi karanci dole mata su hakura a rika auren 4>>Inji Tauraruwar fina-finan Kudu, Bimbo Akintola

Maza sun yi karanci dole mata su hakura a rika auren 4>>Inji Tauraruwar fina-finan Kudu, Bimbo Akintola

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Kudu, Bimbo Akintola ta bayyana cewa, maza sun yi karanci dan haka dolene mata su hakura a rika yin auren mata 4. Tace hakan ne zai kawo saukin dadewar mata da suke yi a gidajen iyayensu ba tare da aure ba. Ta bayyana cewa, bayan haka ma auren mace fiye da daya al'adar Yarbawa ce dan haka ya kamata a ci gaba da dabbaka wannan al'ada.
Gwajin kwayoyin Halitta na DNA dan a gano cewa dan da aka haifa dan miji ne ko dan Zyna ne Haramun ne a musulunci>>Inji Malam Dr. Sharafdeen Gbadebo

Gwajin kwayoyin Halitta na DNA dan a gano cewa dan da aka haifa dan miji ne ko dan Zyna ne Haramun ne a musulunci>>Inji Malam Dr. Sharafdeen Gbadebo

Duk Labarai
Malamin Addinin Musulunci, Dr. Sharafdeen Gbadebo wanda yayi wa'azi da yarbanci ya bayyana cewa, yin Gwajin kwayoyin halitta na DNA haramun ne a Musulunci. Ana yin gwajin DNA ne dan gano da na wanene musamman idan aka samu gaddama tsakanin mata da miji, mijij yana zarginta da kawo mai dan da ba nashi ba. Malamin yace a addini babu tsarin yin gwajin DNA. Yace abinda addini ya zo dashi, rantsuwa ake yi tsakanin matar da mijin.
Kalli Bidiyo: Itama Momi Gombe ta mallaki sabuwar Wayar iPhone 17 pro max ta Miliyoyin Naira

Kalli Bidiyo: Itama Momi Gombe ta mallaki sabuwar Wayar iPhone 17 pro max ta Miliyoyin Naira

Duk Labarai
Rahotanni sun ce Tauraruwar fina-finan Hausa, Momi Gombe ta mallaki Sabuwar Wayar iPhone 17 pro max ta Miliyoyin Naira. An ga Momi tana nuna sabuwar wayar tata inda ake mata kirari. A baya dai Ummi Gayu da Asiya Chairlady ne suka bayyana mallakar wayar a Kannywood. https://www.tiktok.com/@haseenamakeup/video/7556239686914608392?_t=ZS-90CvbYzp2wr&_r=1
Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah ya kawo inda Sheikh Mansoor ya kwatanta Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da hankaka

Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah ya kawo inda Sheikh Mansoor ya kwatanta Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da hankaka

Duk Labarai
Malamin Addinin islama, Sheikh Musa Asadussunnah ya kawo inda Sheikh Mansoor yacewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Hankaka. Sheikh Musa yace Annabi ya bayyana Hankaka da fasikar daba wadda yace ko a Harami aka ganta a kashe, amma Malam Mansur ya kwatanta Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) dashi. https://www.tiktok.com/@malazanna/video/7555398585819352328?_t=ZS-90Csz4hjQNE&_r=1 Malam ya kawo wannan misali ne yayin da ake ci gaba da akaddama kan kalaman Malam Lawal Triumph game da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam).
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji abinda wani mutum yawa diyar dan uwansa da aka bashi riko da ya sa ake ta Allah wadai dashi

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji abinda wani mutum yawa diyar dan uwansa da aka bashi riko da ya sa ake ta Allah wadai dashi

Duk Labarai
Wata mata dake baiwa mata 'yan uwanta shawara kan zama da mazajensu tace, tunda take wannan aiki sau 2 ta taba cewa mace ta bar gidan mijinta. Tace na biyun ya faru kwanannan kuma labarin ya hanata bacci. Ta kara da cewa, Wani mutum ne da yayi aure sai ya dakko diyar wanda ya riketa. Matarsa tace ya rika lalata da yarinyar tin bata kai shekara 10 ba a Duniya yanzu har ta kai shekaru 17 kuma suna da 'ya'ya 4 dashi. Tace abin ya ishetane saboda yarinyar ta raina kowa a gidan kuma ita matar mutumin tana tsoron kada itama awa 'ya'yanta. Ji cikakken labarin a kasa: https://www.tiktok.com/@warakatemple_reviewpage/video/7554487840709610760?_t=ZS-90CJ0gPwAj2&_r=1
Nan da shekarar 2050 yawan ‘yan Najeriya zai karu kuma matsalar tsaro da hakan zai iya haifarwa yafi wanda ake ciki yanzu>>Tsohon Shugaban kasa, Obasanjo yayi gargadi

Nan da shekarar 2050 yawan ‘yan Najeriya zai karu kuma matsalar tsaro da hakan zai iya haifarwa yafi wanda ake ciki yanzu>>Tsohon Shugaban kasa, Obasanjo yayi gargadi

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, yawan 'yan Najeriya da ake da su zai iya karuwa zuwa Miliyan 400 nan da shekarar 2050. Obasanjo ya bayyana hakane yayin bude wani sabon gurin kimiyya da Fasaha a jihar Sokoto. Yace nan da shekaru 25 idan 'yan Najeriya suka karu suna bukatar aikin yi da abinci wanda idan basu samu ba, hakan zai iya kawo matsala. Yace hanya daya ce ta magance wannan matsala itace tun yanzu a baiwa matasa masu tasowa Ilimi. Yace idan kuwa ba haka ba, matsalar tsaron da za'a fuskanta nan gaba tafi wadda ake ciki yanzu.
Majalisar Shura za ta watsa zama da Sheikh Lawal Triumph kai tsaye

Majalisar Shura za ta watsa zama da Sheikh Lawal Triumph kai tsaye

Duk Labarai
Sakataren Majalisar Shura ta Kano, Shehu Wada Sagagi ya ce da farko za a fara da aike masa takardar gayyata tukunna wadda kuma za ta ƙunshi rana da lokacin da zai bayyana a gaban kwamitin. Ya kuma ƙara da cewa domin cire shakku daga zukatan al'umma an shirya yin zaman kai tsaye. "Wannan zama an shirya yin sa ne "Live" wato kai tsaye domin kowa ya ga irin tambayoyin da za a yi masa da kuma irin amsoshin da zai bayar," in ji Shehu Sagagi. Dangane kuma da labaran da ke yawo a kafafen watsa labarai kan cewa Majalisar ta dakatar da Malam Lawal Triumph daga yin wa'azi, sai Shehu Sagagi ya ce a'a ba wai an hana shi yin wa'azi ba ne kwata-kwata. "E an kawo shawara ne cewa wasu mutane suna ta fitintunu ana ta maganganu marasa daɗi har daga wajen jihar da ake ganin wannan abun zai iya ha...