Saturday, May 24
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Watanni 7 bayan da Kotun koli tace a rika baiwa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba tare da sun bi ta hannun gwamnoni ba har yanzu ba’a aiwatar da hukuncin ba

Watanni 7 bayan da Kotun koli tace a rika baiwa kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba tare da sun bi ta hannun gwamnoni ba har yanzu ba’a aiwatar da hukuncin ba

Duk Labarai
Watanni 7 kenan tun bayan da kotun koli ta yi hukunci inda tace a daina baiwa gwamnoni kudaden kananan hukumomi inda tace a rika baiwa kananan hukumomin kudadensu kai tsaye. Saidai har yanzu gwamnatin tarayya bata fara aiwatar da wannan hukunci ba, wanda wasu masana na ganin hakan kin girmama bangaren shari'a ne ganin cewa kotun koli itace kotu mafi girma a kasarnan. Dama dai tun a wancan lokaci, Gwamnoni sun shigar kara inda suka nemi dakatar da hukuncin amma basu yi nasara ba. A ranar July 11, 2024 ne kotun kolin karkashin jagorancin me shari'a Lateef Fagbemi SAN ta yi wannan hukunci. Gwamnatin tarayya a kokarin kawo tsaiko wajan aiwatar da wannan hukunci ta baiwa gwamnatocin jihohi watanni 3 su gudanar da zabukan kananan hukumomi dan fara aiwatar da wannan doka amma shiru ka...
‘Yan Fafutuka na kasashen Yarbawa sun bukaci a kama tsohon shugaban kasa, Janar Babangida a Hukuntashi

‘Yan Fafutuka na kasashen Yarbawa sun bukaci a kama tsohon shugaban kasa, Janar Babangida a Hukuntashi

Duk Labarai
Da yawan 'yan fafutuka na jihohin yarbawa sun nemi da a kama tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida a hukuntashi. Wasu daga cikinsu sun ce a zamanin mulkinsa ya azabtar dasu da iyalansu ya jefa rayuwarsu cikin rashin tabbas. A zamanin mulkin tsohon shugaban kasar da ya faru a tsakanin shekarun 1985 zuwa 1993 an gudanar da zaben Abiola wanda janar Babangida ya soke. Wannan ya jawo hargitsi a wancan lokacin wanda har sai da aka kashe mutane akalla 100, kamar yanda rahotanni suka bayyana. An kuma kama mutane da yawa saboda fitowa zanga-zanga musamman dan nuna rashin amincewa da soke zaben, daga cikin wadanda aka kama akwai Chief Gani Fawehinmi, Alao-Aka-Bashorun, Femi Falana, SAN, Femi Aborisade, Debo Adeniran, Kunle Ajibade. Dan hakane suka hada baki suka ce ba...
Tirr: Gwamna a kasar Amurka ya nemi a daina cewa uwa mahaifiya, a rika ce mata ma’ajiyar Maniyyi

Tirr: Gwamna a kasar Amurka ya nemi a daina cewa uwa mahaifiya, a rika ce mata ma’ajiyar Maniyyi

Duk Labarai
Gwamnan jihar Wisconsin ta kasar Amirka, Tony Evers ya nemi a canja sunan uwa a daina kiranta da mahaifiya a rika kiranta da ma'ajiyar Maniyyi. Ya bayyana hakane a cikin kasafin kudin da ya kai majalisar jiharsa inda ya kuma bukaci a canja sunan mahaifi da mata da miji duka. Saidai da yawan 'yan kasar Amurkar basu yi na'am da wannan shawara tasa ba inda suka rika sukarsa da cewa wannan cin zarafin mahaifiyane.
Mummunan hadari yayi sanadiyyar mùtùwàr Mutane 12, wasu sun jikka a jihar Naija

Mummunan hadari yayi sanadiyyar mùtùwàr Mutane 12, wasu sun jikka a jihar Naija

Duk Labarai
Wani mummunan Hadarin da ya faru a jihar Naija yayi sanadiyyar mutuwar mutane 12 inda wasu kuma suka jikkata. Lamarin ya farune akan titin Agaie zuwa Lapai. Kwamandan hukumar kiyaye hadura ta jihar, FRSC, Kumar Tsukwam ya tabbatarw da manema labarai hakan a sanarwar da ya fitar ranar Asabar a Minna. Yace har yanzu ma'aikatansa na wajan da hadarin ya faru inda yace zasu tattaro bayanai su bayar game da hadarin. Wani da ha shaida yanda abin ya faru, ya gayawa majiyarmu cewa, 3 daga cikin wadanda suka mutu 'yan gida dayane. Sannan sun ce hadarin ya farune a yayin da wata motar Bas ke tafiya daga Minna zuwa Katcha ta yi taho mu gama da wata trela a daidai kauyen Jippo dake kusa da Mashina. Wanda suka jikkata ciki hadda direban suna karbar kulawa a asibitin Lapai General Hospi...
Kalli Bidiyon yanda hukumar NAFDAC ta kama Kwandam(Kwaroron Roba) wanda ya lalace da ake sayarwa da mutane shi

Kalli Bidiyon yanda hukumar NAFDAC ta kama Kwandam(Kwaroron Roba) wanda ya lalace da ake sayarwa da mutane shi

Duk Labarai
A wani abin mamaki da ya faru, an kama wasu dake sayar da kwaroron roba da ya lalace. Suna canja masa mazubine da kuma shekarar da ya kamata ya lalace inda suke sake sayar dashi kamar sabo. Kuma shi wannan kwaroron roba, hukumar kasar Amurka, USAID ce ta bayar dashi kyauta. https://www.youtube.com/watch?v=CpJh-x9vvVk Masana ilimin lafiya sun bayyana cewa, amfani da kwaroron roba da ya lalace zai iya sawa ya huje yayin da ake amfani dashi wanda hakan ka iya kaiwa ga daukar cikin da ba'a shirya ba da muna kamuwa da cutukan da ake dauka a wajan jima'i. Tuni dai hukumomi a ma'aikatar lafiya suka sanar da daukar matakan fara binciken dan gano masu aikata irin wannan ta'asa.
Kamfanin sadarwar Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a kasuwancin sayar da data

Kamfanin sadarwar Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a kasuwancin sayar da data

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kamfanin sadarwa na Airtel ya sanar da tafka asarar Dala Miliyan $344 a wajan kasuwancin sayar da data. Kamfanin yace ta tafka asarar a watanni 9 da suka gabata wanda suka kare a karshen watan Disamba na shekarar 2024. A shekarar baya kamfanin ya samu kudin shiga daga kasuwancin sayar da data wanda suka kai dala miliyan $539. Hakan na faruwane yayin da yawan masu amfani da layin waya na Airtel suka karu wanda a yanzu sun kai Mutane Miliyan 56.6. Shugaban kamfanin, Dinesh Ba...
Jam’iyyar PDP ta lashe gaba dayan zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Osun

Jam’iyyar PDP ta lashe gaba dayan zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Osun

Duk Labarai
Rahotanni daga zaben kananan hukumomin jihar Osun da ya gabata ya nuna cewa, Jam'iyyar PDP ce ta lashe zaben a kafatanin kananan hukumomin jihar. Kwamishinan zabe na jihar, Hashim Abioye ne ya bayyana hakan bayan kammala zaben inda yace PDP ce ta yi nasara a kananan hukumomi 30 da mazabu 323 dake fadin jihar. Yace an samu nasarar kammala zaben cikin nasa. Yace Jam'iyyu 18 ne suka yi takara a zaben kuma PDP ce ta lashe zaben na kananan hukumomi dana kansiloli baki daya.
An kama magidanci da Abokinsa da sukawa Agolarsa fyàdè, suka dirka mata ciki

An kama magidanci da Abokinsa da sukawa Agolarsa fyàdè, suka dirka mata ciki

Duk Labarai
Mahukunta a jihar Legas sun kama magidanci dan kimanin shekaru 38 da abokinsa da suka hadu sukawa agolarsa me shekaru 14 fyade. Kakakin 'yansandan jihar, CSP Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar hakan a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Asabar. Ya kara da cewa, mahaifiyar yarinyarce ta kai koke a ofishin 'yansanda dake yankin Okokomaiko na jihar. Rahoton yace sun dirkawa yarinyar ciki inda a yanzu tana dauke da cikin wata 9. Ya kara da cewa, da zarar an kammala bincike, za'a gurfanar da wanda ake zargin a kotu.