An Gabatar Da Kasar Karatun Kur'ani Na Jami'an Tsaron Nijeriya Baki Daya A Jami'ar Alkalam Dake Katsina
Abun dai sai wanda ya gani, gaskiya sun zuba capacity wajen karanta kur'ani me girma.
Daga Khalid Yusuf Sambo
Rundunar ƴansandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama ƴansandan bogi uku da ake zargi da yin damfara ta hanyar shigar burtu a matsayin ƴansanda a jihar Kano, bayan sun damfari wani mutum naira miliyan ɗaya da dubu talatin.
Mutanen da aka kama sun fito ne daga ƙaramar hukumar Daura ta jihar Katsina inda aka kama su a ranar 2 ga Satumba, 2025, a Danagundi Quarters.
Rundunar ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da Jama’a na ƴansanda, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar.
Sanarwar ta ce "Kamar yadda bincike ya nuna, an kama su ne bayan wanda suka damfara ya nemi ɗauki, inda ya yi bayanin yadda abin ya faru.
"Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargi sun yi shigar burtu a matsayin ƴansanda inda suka yi iƙirarin cewa suna da wasu ƙwarewa na musamman da za su t...
Babban Sifeton Ƴansandan Najeriya, Kayode egbetokun ya naɗa CSP Benjamin Hundeyin a matsayin sabon mai magana da yawun rundunar ƴansandan ƙasar (FPRO)
Naɗin Hundeyin na ƙunshe cikin wata sanarwa da kakakin rundunar mai barin gado, Muyiwa Adejobi ya fitar.
”Babban Sifeton ƴansandan ya buƙace shi da aiki da ƙwarewarsa ta sadarwa wajen inganta aikin ɗansanda a Najeriya ta hanyar ƙarfafa hulda da jama'a,'' in ji sanarwar.
Kafin sabon muƙamin, CSP Benjamin Hundeyin ya kasamnce kakain rundunar ƴansanda reshen jihar Legas, inda ya kwashe shekaru yana wannan aiki.
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kama hanyar zuwa kasashen Faransa da Ingila inda zai yi hutu acan.
Gwamnan Imo dana Legas da sakataren Gwamnatin tarayya na daga cikin wadanda suka mai rakiya zuwa filin jirgin.
Fadar shugaban kasa tace shugaban zai kwashe kwanaki 10 ne yana wannan hutun.
https://twitter.com/NTANewsNow/status/1963593117988200540?t=gFM_kzD3OO7721pi9xO8VQ&s=19
Rahotanni daga jihar Kaduna sun bayyana cewa, 'yansanda sun kulle ofishin jam'iyyar ADC a jihar yayin da kungiyar ke shirin gudanar da taro.
Wasu daga cikin 'yan jam'iyyar sun hau kafafen sada zumunta suna bayyana mamaki da rashin jin dadinsu.
""An Jibge Jami'an Tsaro Sama Da Mota 20 Domin A Hanamu Taron Da Zamuyi Ayau" A Ofishin Jami'iyyar ADC Dake Kan Titin Ali Aƙilu.
Wacce irin siyasa akeyi haka a jihar Kaduna?, anata amfani da jami’an tsaron da'aka samar domin tsare ƙimar Demokraɗiyya ana yiwa Demokraɗiyyar fyaɗe. sannan a turo wasu wanda basufi ƙarfin cikinsu ba, wanda da ƙyar suke iya biyan kudin haya, suzo media suna kare ƙarya da zalunci.
Ance an kashe adawa a jihar Kaduna, to kenan me ake tsoro tunda an kashe adawa?, Allah ya kyauta" Inji Comrades DanHabu
""An Jibge...
Ƙungiyar dattawan Arewacin Najeriya (NEF) ta buƙaci shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a yankin sakamakon matsalar tsaro da ke ci gaba da ta'azzara wanda ya lalata rayuka da tattalin arzikin ƙasar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere ya fitar, ƙungiyar ta bayyana damuwarta kan hare-hare da garkuwa da mutane da kashe su ba ƙaƙautawa da ake ci gaba da yi a yankin.
Ya yi gargaɗin cewa idan ba a magance matsalar ba, alummomi ka iya ɗaukar matakin kare kai wanda zai iya kai wa ga ƙazancewar rikicin da kuma kawo cikas ga dimokraɗiyyar ƙasar da zaman lafiyar yankin.
"Muna kuma yi kira ga gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai da dama ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci domin ƙara duba girman lamarin, kuma ta aika jam'ian tsaro masu...
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce muhimman tsare-tsaren gwamnatinsa sun soma samar da sakamakon da ake buƙata, inda ya ce tattalin arziƙin ƙasar ya daidaita har ya soma janyo hankalin masu zuba jari daga ƙasashen duniya.
Tinubu ya faɗi hakan ne a fadar sa da ke Abuja, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, a lokacin da ya karbi baƙuncin Oba Ghandi Afolabi Oladunni Olaoye, Orumogege III na Ogbomoso da tawagarsa.
A cewar shugaban, halin ko-in-kula da rashawa da fasa kauri da yaudara ne su ka hana Najeriya samun kuɗaɗen shiga da za a yi amfani da shi wajen samar da ci gaba.
''Tattalin arziƙinmu ya fuskanci barazana, wajibi ne mu ɗauki matakai ƙwarara. Amma tare da adduo'in ku da haƙuri da juriyarku, ina farin cikin shaida muku cewa a yanzu tattalin arziƙi ya dai-daita'...
Wata sanarwa daga fadar shugaban Najeriyar, ta ce Shugaba Bola Tinubu zai fara hutun ne daga ranar Alhamis, 4 ga watan Satumban 2025.
Sanarwar ta kuma ce Tinubu zai shafe tsawon kwana 10 a Faransa da Ingila kafin ya koma Najeriya.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya bayar da labarin cewa, a wasu lokutan jami'an tsaro na kallo wasu abubuwan ke faruwa amma sai su ce wai ba zasu iya daukar mataki ba suna jiran umarni daga sama.
Ya bayyana hakane yayin hira da manema labarai.
Dauda yace wasu lokutan har kuka yake.
Yace abin takaici duk inda wani shugaban 'yan Bindiga yake a jiharsa ya sani kuma duk inda zasu yana sane amma babu abinda zai iya yi.
https://twitter.com/AM_Saleeeem/status/1963549967643034005?s=19
Dan majalisar tarayya daga jihar Kano, Abdulmumin Jibrin ya bayyana cewa, Yana goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce a shekarar 2027.
Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV.
Yace dalilinsa shine yana son kamar yanda Arewa ta yi shekaru 8 akan mulki, itama kudu ta kammala shekaru 8.
Yace yana mamakin dan Arewa ya rika cewa an cuci Arewa a tsarin karba-karba na mulki a Najeriya.
https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1963321987444424770?t=xvm4haloRuAuSdXvW_n7uQ&s=19