Kamfanin kere-kere na sojojin Najeriya, DICON ya bayyana Bindigar yaki ta farko da ya kera.
Kamfanin ya bayyana hakane a matsayin ci gaba da kuma rage dogaro da kasashen waje waja samar da makamai.
Masu sharhi na bangaren tsaro sun bayyana cewa, wannan ba karamin ci gaba bane.
'yan Najeriya da yawa sun bayyana farin ciki da wannan labari inda suka ce ya kamata a samar da Bindigar da yawa ta yanda sojoji zau rika amfani da ita wajan yaki.
Daliba a Kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar kogi, Omotosho Dorcas me shekaru 26 ta rigamu gidan gaskiya a kokarin zubar da cikin gaba da fatiha da ta yi.
Lamarin ya farune a ranar 26 ga watan Augusta a Asibitin Al-Hassan Clinic and Maternity dake Lokoja.
Kafar zagazola makama tace Dorcas na dauke da cikin watanni 6 ne onda taje asibitin a zubar mata dashi wanda anan aka samu matsala ta rasu.
'Yansanda sun je waja inda suka dauki hotuna aka kai gawarta Mutuware sannan aka kama masu hannu a lamarin.
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo gida Najeriya daga kasar Brazil inda yaje halartar taron ci gaban kasashen Afrika.
Shugaba Tinubu ya taso daga kasar Brazil da misalin karfe 12 na kasar ranar Laraba, inda ya zo Najeriya ranar Alhamis kamar yanda me magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya bayyana.
Manyan jami'an gwamnati ne suka tarbi shugaban kasar a filin jirgin sama na Abuja.
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false}
Wannan wata matace data bayyana cewa, matar wanda ke son aurenta tana ta mata barazana da cewa, ta rabu dashi.
Saidai tace a gefe daya kuma gashi ya siya mata mota.
https://www.tiktok.com/@sweet_asmee3/video/7542290114689453313?_t=ZS-8zEs7VhCa9Y&_r=1
Tauraruwar Tiktok, Nafisa Ishak ta koka da cewa sabon kalubalen da suke fuskanta shine wai Breziya ta kai dubu bakwai.
Ta bayyana hakane a shafinta na Tiktok inda tace 'yan mata su rika amfani da leda.
Tace kwanannan za'a fara ganin 'yan mata babu rigar nono:
https://www.tiktok.com/@nafisa_ishak/video/7543269637975248146?_t=ZS-8zErVYbNeFs&_r=1
Matar tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ta dauki hankula sosai saboda rawar da ta yi a shafinta na Tiktok.
Matar ta yi rawa sosai inda aka ga tun tana zaune sai da ta tashi tsaye.
https://www.tiktok.com/@maryamnikicminaj/video/7542982337257082132?_t=ZS-8zEpbHO9sDh&_r=1
Da yawa dai sun rika fadin itama ta zama irinsa.
Kotu a kasar Equatorial Guinea ta daure dan shugaban kasar me suna Ruslan Obiang Nsue saboda sayar da jirgin shugaban kasar.
An masa daurin shekaru 6 ne a ranar 26 ga watan Augusta na shekarar 2025.
Saidai yana da zabin ya biya takarar $255,000 maimakon daurin gidan yarin.
Bidiyo ya bayyana dake nuna cewa, a watan Yuni an bayyana yanda aka sace karafan dake rike da titin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna amma ba'a dauki mataki ba.
A jiya ne dai jirgin kasan yayi hadari inda mutane 6 suka jikkata sannan wani mutum daya ya rasu kamar yanda rahoton ya nunar.
A Bidiyon an ga yanda wani ke nuna karafan jirgin kasan a kwance babu wani karfe dake rike dasu.
https://twitter.com/SasDantata/status/1960709922456240269?t=1GmcdDRXOxRusyElFRE9HQ&s=19
Yau Jihar Jigawa Take Murnar Cika Shekaru 34 Da Kirƙirar Ta, Inda Ayyukan Tsohon Gwamna Sule Lamido Suka Karaɗe Kafofin Sada Zumunta Musamman A Tsakanin 'Yan Jihar
Ko kuma kuna da Gwamnan da kuka fi tunawa da shi a jiharku a lokacin irin wannan ranaku?
Daga Abubakar Shehu Dokoki