Friday, May 23
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Wata Sabuwa, an shigar da karar neman tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu daga kan kujerarsa saboda cin zalin ‘yan kasa

Wata Sabuwa, an shigar da karar neman tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu daga kan kujerarsa saboda cin zalin ‘yan kasa

Duk Labarai
Wani lauya me rajin kare hakkin al'umma, Mr. Olukoya Ogungbeje ya kai karar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda yace ya take hakkin 'yan kasa. Ya kai karar Tinubu ne babbar kotun tarayya dake Abuja inda yace Tinubun yana take hakkin 'yan kasa da murkushesu a duk sanda suka yi yunkurin nuna rashin jin dadin mulkinsa ta hanyar zanga-zanga. Ya kawo musalin Zanga-zangar da aka yi a watan Agusta na shekarar data gabata inda yace Gwamnatin Tinubu ta murkushe masu zanga-zangar da take hakkinsu na 'yan kasa. A cikin wadanda yake karar hadda babban lauyan Gwamati kuma Ministan shari'a, Prince Lateef Fagbemi inda yace yana neman kotu ta baiwa majalisar tarayya umarnin fara shirin tsigesu duka daga mukamansu saboda laifukan da suka aikata sun bada damar a tsigesu. Saidai lauyan Shugaban...
Kamar dai yanda suka rika fadi akan Tallafin Man Fetur, Gwamnatin tarayya tace wasu kalilanne ke amfana da tallafin wutar lantarki

Kamar dai yanda suka rika fadi akan Tallafin Man Fetur, Gwamnatin tarayya tace wasu kalilanne ke amfana da tallafin wutar lantarki

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa tana biyan Naira Biliyan 200 a matsayin tallafin wutar lantarki duk wata. Kuma tace wasu kalilanne da basu wuce kaso 25 cikin 100 na al'umma ba ke amfana da wananna tallafi inda tace talafin baya kaiwa ga wadanda ya kamata. Babbar me baiwa shugaban kasa shawara akan makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana hakan a ranar Litinin. Ta yi maganane akan rahoton dake cewa za'a kara farashin wutar lantarki da kaso 65 cikin 100. Tace maganar da tayi ba'a fahimceta ba, tace abinda ta fada shine kudaden da 'yan Najeriya ke biya na wutar lantarki suna biyan kaso 65 cikin 100 ne inda gwamnati ke biya musu sauran. Tace amma mafi yawa, masu kudi ne kalilan suka fi amfana da wannan tallafi na wutar lantarkin. Game da karin kudin wuta da kuma zargin cewa ...
Babu maganar tattaunawa, ba zamu rage ko sisi a karin kudin kiran da muka yi ba>>Kamfanonin Sadarwa Irin su MTN, Airtel suka bayyana

Babu maganar tattaunawa, ba zamu rage ko sisi a karin kudin kiran da muka yi ba>>Kamfanonin Sadarwa Irin su MTN, Airtel suka bayyana

Duk Labarai
Kungiyar kamfanonin sadarwa ta bayyana cewa babu wani abu da zai sa su rage karin farashin kudin kiran waya da kaso 50 da gwamnati ta amince musu. Kamfanonin sun nemi yin karin kaso 100 bisa 100 amma hukumar sadarwa ta NCC ta amince musu da yin karin kaso 50 cikin 100. Wannan karin ne yasa kungiyoyin fafutuka suka ce basu amince dashi ba dan zai saka mutane a cikin wahala. Saidai shugaban kungiyar masu kamfanonin sadarwa ta Najeriya Gbenga Adebayo yace ba zasu rage ko sisi a cikin kaso 50 din da suka kara ba. Yace ragin zai zama kamar mutum ne dake bukatar numfashi amma a ki bashi, yace muddin ana son ci gaba da samun sabis me karfi da dorewa da kuma kara fadada ayyukansu to sai an bari an yi wannan kari.
Da Duminsa: Kungiyar kwadago ta NLC ta fasa zanga-zanga kan karin kudin kiran waya

Da Duminsa: Kungiyar kwadago ta NLC ta fasa zanga-zanga kan karin kudin kiran waya

Duk Labarai
Kungiyar kwadago ta NLC ta fasa yin zanga-zanga data shirya kan karin kudin kiran waya da kaso 50. A ranar Talata ne dai Kungiyoyin na kwadago da sauran na fafutuka suka shirya zanga-zanga dan nuna adawa da wannan kari. kungiyoyin sun bayyana dakatar da zanga-zangar ne bayan ganawa da wakilan Gwamnatin tarayya a ranar Litinin a ofishin Sakataren gwamnatin tarayya a Abuja. Shugaban kungiyar kwadagon Joe Ajaero yace sun dakatar da zanga-zangar ta yaune saboda gwamnati ta amince ta kafa kwamiti na musamman da zai duba kowane bangare dan samar da mafita akan lamarin.
Da Duminsa:Shugaba Tinubu ya amince da kafa jami’ar Kimiyyar Muhalli a Ogoni jihar Rivers

Da Duminsa:Shugaba Tinubu ya amince da kafa jami’ar Kimiyyar Muhalli a Ogoni jihar Rivers

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa kudirin dokar kafa jami'ar kimiyyar Muhalli a Ogoni dake jihar Rivers, Niger Delta. Shugaban ya sakawa dokar hannu ne a fadarsa dake Abuja da yammacin ranar Litinin. Shugaban yace wannan babbar nasara ce a kokarin Najeriya wajan kawo ci gaban muhalli, Ilimi, da ci gaba me dorewa. Yace wannan jami'a na nuni da cewa gwamnati ta damu da ci gaban al'ummar yankin gaba daya inda yace shekaru da yawa mutanen yankin na ta fafutukar ganin sun samawa kansu mafita ta bangaren gyaran muhalli. Shugaban ya kuma jinjinawa majalisar tarayya bisa kokarin amincewa da wannan kudirin dokar. Ya kuma jawo hankalin masu ruwa da tsaki da suka hada da matasa, iyaye, da masu zaman kansu da su goyawa wannan jami'a baya.
Ji abinda Ma’aikatan hukumar KNUPDA na Kano suka yi bayan kkisan mutane 4 a Kano

Ji abinda Ma’aikatan hukumar KNUPDA na Kano suka yi bayan kkisan mutane 4 a Kano

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, ma'aikatan hukumar KNUPDA dake kula da gidaje a Kano sun tsere daga ofisoshinsu bayan kisan mutane 4 a Rimin Auzinawa, Ungoggo, Jihar Kano. Gidaje kusan 40 ne aka sakawa fentin rusau. Jaridar Daily Trust tace ta kai ziyara hukumar dan tattaunawa da jami'anta dan jin ba'asin yanda lamarin ya faru amma bata iske kowa ba sai ma'ikaci daya. Kuma ya shaidawa jaridar cewa, tsoron kawowa hukumar harine yasa ma'aikatan hukumar suka tsere suka dauke motoci da sauran ababen hawansu. Jaridar ta Daily Trust ta kuma kara ruwaito cewa, jami'in hukumar ta KNUPDA ya shaida mata cewa, ba sune suka je suka yi wancan rusau din ba da ya jawo asarar rayuka.
Kalli Bidiyon yanda jami’an tsaro suka kkashe mutane 4 a Rimin Auzinawa Kano,”Abba kaci Taliyar Karshe”

Kalli Bidiyon yanda jami’an tsaro suka kkashe mutane 4 a Rimin Auzinawa Kano,”Abba kaci Taliyar Karshe”

Duk Labarai
Wannan bidiyon yanda lamarin rikicin rusau ya faru ne a jihar Kano inda Rahoton Daily Trust yace jami'an tsaro sun kashe mutane 4. Lamarin ya farune a Rimin Auzinawa inda aka rushe gidajen mutane su kuma suka mayar da martani ta hanyar jifar jami'an tsaron. https://twitter.com/Mk__maitama/status/1886337089412714757?t=zdl2zRvXaG1ctDykEILFMw&s=19 Su kuma jami'an tsaron sun bude wuta inda hakan yayi sanadiyyar kisan mutane 4. Kalli Bidiyon faruwar lamarin anan

Maganin ulcer sadidan

Magunguna
A wannan rubutu, zamu yi bayanin ciwon gyambon ciki watau Ulcer, saidai kamin mu fara bayani, muna da maganin ulcer sadidan wanda da yardar Allah ana warkewa, ga wanda yake da bukata yana iya yi mana magana a wannan lambar ta WhatsApp ko a kira, 09070701569 muna turawa duka jihohin Najeriya. Da farko Menene Ulcer? Ulcer ko Gyambon Ciki, wani ciwo ne ko kumburi dake faruwa a cikin hanjin mutum. Yawanci yana taba abinda ke da alaka da hanjin cikin mutum ne. Alamomin ulcer Alamomin ulcer sun hada da, jin zafi a cikin ciki dake dadewa zuwa wasu awanni ko a ji shi na dan lokaci kadan. Wasu kan daina jin zafin a yayin da suka daina cin abinci ko suka sha magani. Wata ulcer din sai tsakar dare tako tasowa mutum ko yayin da yake cikin cin abinci. Ana iya samun sauki ta hanyar ...
Kalli Bidiyon cikakkiyar hirar da aka yi da matar marigayi Albani Zaria

Kalli Bidiyon cikakkiyar hirar da aka yi da matar marigayi Albani Zaria

Duk Labarai
Matar marigayi Sheikh Albani Zaria ta fito ta yi cikakken bayani kan matsalar da suke ciki game da 'yan damfara da kuma daliban malamin. A wani Bidiyo da ya yadu sosai a kafafen sada sumunta, an ga me dakin Albani tana zubar da hawaye saboda bakin cikin da ta samu kanta a ciki. https://youtu.be/3U7poakQT3k?si=uqg92n2W86Sf8Kn8 Da yawan mutane sun tausayawa iyalan malam inda aka rika tambayar ina dalibansa da sauran malamai 'yan uwansa? Kalli Bidiyon anan