Saturday, December 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Sheikh Gumi ya gargadi Shugaba Tinubu inda ya fallasa wani shiri na yunkurin aika malamai Lahira

Sheikh Gumi ya gargadi Shugaba Tinubu inda ya fallasa wani shiri na yunkurin aika malamai Lahira

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya fallasa cewa akwai jami'an leken Asiri na kasar Israel, watau mossad a Najeriya. Ya kuma yi zargin cewa, akwai yiyuwar kisan Malamai a shigowar Mossad Najeriya. Malam ya bayyana hakane ta shafinsa na sada zumunta inda yace barin Mossad su samu karfi a Najeriya ba alheri bane. Sheikh Gumi ya bayar da misali da mutuwar tsohon shugaban kasa, General Sani Abacha inda yace akwai zargi mutuwarsa, domin ya mutu ne jim kadan bayan ganawa da yasir Arafat tsohon shugaban Falasdinawa. Gumi yace duk wanda ya baiwa shugaban kasar shawarar hada kai da kasar Israela bai bashi shawara me kyau ba. Ya ce ta yaya ma kasa Irin Israyla me kisan kiyashi za'a bada daa ta shigo Najeriya?
Gwamnatin tarayya tace zata rama tsaurara Yin Bizar da kasar Amurka ta kakabawa ‘yan Najeriya

Gwamnatin tarayya tace zata rama tsaurara Yin Bizar da kasar Amurka ta kakabawa ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin kasar Amurka tace duk dan Najeriyar dake neman Visa ta shiga kasarta dolene ya nuna yanda yake amfani da kafafen sadarwa na tsawon shekaru 5 baya. Dokar tace kin yin hakan zai iya sa a hana mutum Visar shiga kasar Amurkar. Saidai cikin gaggawa, Gwamnatin taraya ta sha Alwashin daukar irin wannan mataki akan 'yan kasar Amurka masu shigowa Najeriya. Kasar Amurka ta bayyana wannan sabuwar dokane ta kafar X wanda tace hakan na daga cikin shirin shugaban kasarta, Donald Trump na ganin ya samarwa kasar tasa tsaro. Me magana da yawun ma'aikatar tsaro ta Najeriya, Kimiebi Ebienfa ya bayyana cewa, Gwamnatin kasar Amurka tuni ta sanar dasu wannan shiri. Yace itama Najeriya zata dauki irin wannan mataki akan 'yan kasar Amurka masu neman Visa a Najeriya.
KATSINA BA KORAFI: Kalli Yanda Gwamna Dikko Radda Ke Dauke-Dauken Hotuna A Inda Yake Hutu A Kasar Waje

KATSINA BA KORAFI: Kalli Yanda Gwamna Dikko Radda Ke Dauke-Dauken Hotuna A Inda Yake Hutu A Kasar Waje

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} KATSINA BA KORAFI: Gwamna Dikko Radda Ne Ke Dauke-Dauken Hotuna A Inda Yake Hutu A Kasar Waje
Albashin ‘Yan siyasa yayi kadan, inji Gwamnatin tarayya inda tace zata musu karin Albashin

Albashin ‘Yan siyasa yayi kadan, inji Gwamnatin tarayya inda tace zata musu karin Albashin

Duk Labarai
Hukumar kula da albashin ma'aikata, RMAFC ta bayyana cewa tana shirin karawa 'yan siyasa albashi inda tace Albashin nasu yayi kadan musamman lura da irin hidimar da 'yan siyasar kewa Al'umma. Shugaban hukumar, Mohammed Shehu ne ya bayyana hakan a yayin wani jawabi A Abuja ranar Litinin inda yace a yanzu haka albashin shugaban kasa Naira Miliyan 1.5 ne sannan albashin Ministoci kasa da Naira Miliyan 1 ne kuma tun shakerar 2008 ba'a musu karin Albashin ba. Yace abin mamaki ne ga mutane da yawa ace wai shugaban kasar Najeriya me mutane Miliyan 200 ace ana biyansa Albashin Naira Miliyan 1.5 a wata. Yace ba zai yiyu ace Minista ana bashi Albashin Kasa da Naira Miliyan 1 ba sannan ace ba zai yi sata ba, yace ba zai yiyu ace ana biyan Gwamnan CBN da sauran manyan jami'an gwamnati albashi...
Tinubu ya naɗa shugaban PenCom

Tinubu ya naɗa shugaban PenCom

Duk Labarai
Tinubu ya naɗa shugaban PenCom Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa Opeyemi Agbaje, tsohon Mataimakin Babban Manaja (AGM) na bankin GTBank, a matsayin sabon shugaban Hukumar Kula da Fensho ta Ƙasa (PenCom). Agbaje ya taɓa zama Daraktan Gudanarwa a Metropolitan Bank kafin ya bar harkar banki. TheCable ta rawaito cewa wannan naɗin ya zo ne bayan wa’adin kwanaki bakwai da Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) ta bayar, inda ta nemi a gaggauta sake kafa hukumar gudanarwa ta PenCom, tare da yin gargaɗin shiga yajin aiki idan gwamnati ta ƙi bin umarnin. A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, an bayyana shi a matsayin masani mai tasiri a fannoni na kasuwanci, tattalin arziki da manufofin gwamnati. Agbaje ya kammala karatu a Jami’ar Ife (wanda yanzu ake kira Jami’ar Obafemi Awolowo)...
Ku Daina Ɗaukar Abin Da Gwamnoninku Suke Muku Kamar Alfarma Ce, Ko Taimakonku Suke, Haƙƙinku Ne, Cewar Barista Ɗantani

Ku Daina Ɗaukar Abin Da Gwamnoninku Suke Muku Kamar Alfarma Ce, Ko Taimakonku Suke, Haƙƙinku Ne, Cewar Barista Ɗantani

Duk Labarai
Fitattaccen lauya mai rajin kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya, Barista Hamza Nuhu Ɗantani, ya ja hankalin al'umma da su daina kallo ko ɗaukan abubuwan da ƴan siyasa ko shugabanni suke musu a matsayin taimako ko wata alfarma domin ba da kuɗinsu suke yin ayyukan ba. Barista Ɗantani wanda ya wallafa hakan a shafinsa na Facebook, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito, ya fara ne da cewa, "Ba fa noma ko wani aiki suka yi aka biya su suke muku aiki da kuɗin ba! Ba Kuɗinsu ba ne! Ba Dukiyarsu Ba ce! Ba Guminsu ba ne! Su da kansu suka fito suka roƙe ku don ku zaɓe su! Suka dinga manna hotunansu (Posters), suna ta ihu suna shiga lungu da saƙo suna barar ƙuri’unku don kawai su riƙe amanar Dukiyarku!". Inji shi. Barista Ɗantani, ya ci gaba da cewa, "Ku sani Haƙƙinku ne, ba fa kuɗinsu ba ne, ba du...