Thursday, April 30
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Darajar Naira ta yi rugu-rugu a kasuwar Chanji

Darajar Naira ta yi rugu-rugu a kasuwar Chanji

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Darajar Naira ta yi rugu-rugu a kasuwar Chanji. A wani bincike na tsanaki da aka yi, an gano cewa, Nairar ta fadi a tsakanin 14 zuwa 21 na watan Maris na shekarar 2025. Sannan a kowane sati tana rasa darajar Akalla Naira 18.96. A ranar Juma'ar data gabata, an kulle kasuwar Chanji Naira na da farashin N1,536.89. Wannan a kasuwar Gwamnati kenan. Saidai a kasuwar bayan fage, an kulle kasuwar Naira na da farashin N1,580 akan kowace dala. Wannan bayanai duka an samosu ne daga bayanan canjin kudi daga rubun ajiyar bayanai na babban bankin Najeriya, CBN.
2027: Hadakar Atiku da El-Rufai da Obi ba za ta iya kayar da APC ba — Shekarau

2027: Hadakar Atiku da El-Rufai da Obi ba za ta iya kayar da APC ba — Shekarau

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, ya bayyana cewa babu wata haɗakar ‘yan siyasa da za ta iya sauke Shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027. Matsayar Shekarau na zuwa ne kasa da sa’o’i 48 bayan wasu manyan ‘yan siyasa daga jam’iyyun adawa, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da ɗan takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, suka soki matsayar Gwamnatin Tarayya game da rikicin siyasa a Jihar Ribas a wani taron manema labarai da suka gudanar a Abuja. A wata sanarwa da Dr. Sule Yau ya fitar a madadin Shekarau, ya jaddada cewa, sabanin abin da wasu ke hasashe, wannan haɗaka kawai wata tarayya ce ta masu niyyar tsayawa takarar shugaban ƙasa ko mataimakin shugaban ƙasa, ku...
A yanzu Kotu ta amince a yiwa Sanata Natasha Akpoti kiranye

A yanzu Kotu ta amince a yiwa Sanata Natasha Akpoti kiranye

Duk Labarai
Babbar Kotun tarayya dake Lokoja ta amince a shiryawa sanata Natasha Akpoti kiranye. Kotun tace mutanen mazabar Sanata Natasha Akpoti suna da 'yancin yi mata kiranye kamar yanda kundin tsarin mulki ya basu dama. Kotun tace mutanen mazabar zasu iya ci gaba da gudanar da zaben kiranyen da suke shiryawa Sanata Natasha Akpoti amma su bi doka da oda wajan yin hakan. Kotun ta bayyana hakane bayan da a ranar Alhamis tace a dakata da maganar yiwa Sanata Natasha Akpoti kiranye.
Dakatar da gwamnan Rivers ɓata sunan Najeriya ne a idon duniya — Jonathan

Dakatar da gwamnan Rivers ɓata sunan Najeriya ne a idon duniya — Jonathan

Duk Labarai
Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya soki dakatar da gwamnan jihar Rivers da mataimakiyarsa da ƴanmajalisar dokokin jihar, wanda shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi. Jonathan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a matsayin shugaban taro wanda gidauniyar Haske Satumari ta shirya a ranar Asabar a Abuja, inda ya bayyana rashin jin daɗinsa kan matakin na cire zaɓaɓɓun shugabanni. "Wannan matakin da aka ɗauki zai ɓata sunan Najeriya ne a idon duniya," in ji shi, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito. Jonathan ya ce duk da cewar akwai buƙatar ɗaukar matakan da za su magance rikicin siyasar da ya dabaibaye jihar Rivers na tsawon lokaci, a cewarsa dakatar da waɗanda mutane suka zaɓa a matsayin shugabanninsu bai dace ba. Ya ƙara da cewa ya san bai kamata a matsa...
Dalilin da ya sa Gwamnatin Tarayya ba ta fara biyan kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba – ALGON

Dalilin da ya sa Gwamnatin Tarayya ba ta fara biyan kananan hukumomi kudadensu kai tsaye ba – ALGON

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ba ta fara bayar da kudaden kasafi kai tsaye ga Kananan Hukumomi ba saboda ana ci gaba da bin wasu hanyoyin aiki, in ji Kungiyar Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON). Shugaban kwamitin amintattu na ALGON, Odunayo Alegbere, ya bayyana hakan a ranar Juma’a a Abuja bayan wani taron kungiyar. Ya bayyana cewa an umarci kananan hukumomi da su bude asusu a Babban Bankin Najeriya (CBN) domin saukaka aiwatar da tsarin rabon kudade kai tsaye. Duk da cewa har yanzu ba a kammala tsarin ba, Alegbere ya jinjinawa Gwamnatin Tarayya kan ci gaban da aka samu, yana mai cewa hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi babbar nasara ce. Ya jaddada cewa gwamnati na aiki don aiwatar da wannan hukunci, wanda ya hada da ‘yancin gudanarwa da kuma ‘yancin siyasa...
Dalilan da ya sa mata ke rububin rigar mama ta gwanjo a Legas

Dalilan da ya sa mata ke rububin rigar mama ta gwanjo a Legas

Duk Labarai
Bukatar rigar mama ta ganjo a wajen matan Legas na Karuwa, inda hakan ya kasance abin dubawa a jihar, kamar yadda jaridar Vanguard ta rawaito. Wasu mata da jaridar ta zanta da su sun nuna cewa zaɓinsu na rigar mama ya dogara ne kan dalilai kamar araha da kuma ƙarko. Da yawan matan Legas na sayen rigar mama ta gwanjo, wacce aka fi sani da "Okrika" saboda suna samuwa da yawa, ga araha, kuma su na da kyau. Vanguard ta gano cewa baya ga manyan kasuwanni kamar Tejuosho, Balogun, da Katangowa a Legas, ana iya samun rigar mama na Okrika a ƙananan kasuwanni, shaguna, da wuraren masu sayar da kaya a gefen hanya. Mrs Peace Okeke, wadda ake kira "Lady Bra" a tsakanin kwastomominta a Festac Town, yankin Amuwo Odofin, ta ce ta kwashe fiye da shekaru 18 ta na wannan sana'a. A cewarta, tun...
An yi gàrkùwà da soja da wasu sauran mutane a Abuja

An yi gàrkùwà da soja da wasu sauran mutane a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja na cewa an yi garkuwa da wata sojar ruwa dake aiki a hedikwatar tsaro ta kasa tare da wasu mutane. Lamarin ya farune a Mpape dake Abuja ranar Juma'a inda aka shiga har gida aka tafi da wadanda aka yi garkuwar dasu. Wata majiya ta shaida cewa, wadanda aka yi garkuwa dasu din an kira iyalansu inda ake neman Naira Miliyan 100 a matsayin kudin Fansa. Jimullar mutane 3 ne aka yi garkuwar dasu, ciki hadda sojar me suna Lt. Cynthia Akor. Hukumomin soja dai basu ce uffan kan lamarin ba.