Wednesday, April 1
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bidiyo Da Duminsa: An gano hadimin shugaba Tinubu na munafurtarsa wajan kitsa yanda zai fadi zabe a 2027

Bidiyo Da Duminsa: An gano hadimin shugaba Tinubu na munafurtarsa wajan kitsa yanda zai fadi zabe a 2027

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Aliyu Audu ya bayyana cewa dalilin da yasa ya sauka daga mukamin me baiwa shugaban kasar shawara ta musamman shine yana munafurtar shugaban kasar. Yace ba zai yiyu ya ci gaba da zama a gwamnatin Tinubu ba bayan yasan cewa, yana kitsa yanda zai fadi zabe a shekarar 2027. Aliyu ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV inda kuma ya nanata cewa lallai zasu kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a za...
Bidiyo: Ji Tonon Silili yanda shugabar Bankin Fidelity Bank tace ta biya Naira Biliyan 5 dan kada ‘yan sanda su kamata bayan zarginta da cinye makudan kudade

Bidiyo: Ji Tonon Silili yanda shugabar Bankin Fidelity Bank tace ta biya Naira Biliyan 5 dan kada ‘yan sanda su kamata bayan zarginta da cinye makudan kudade

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani Bidiyo ya bayyana na shugabar Bankin Fidelity Bank, Onyeali-Ikpe inda take cewa ta biya Naira Biliyan 5 dan kada 'yansanda su kamata. Hakan na zuwan bayan da ake zarginta da satar ko cinye ko aikata zamba da Naira ₦19Billion. https://twitter.com/SaharaReporters/status/1934547138106786223?t=ToB34Rrj9DdOxiFVwZGjnQ&s=19 A baya ma dai an zargi wata magumagu bayan ganin an cireta daga cikin sunayen wadanda ake zargi da rashawa da cin hanci.
Najeriya na son siyo irin wadannan jiragen 12 daga kasar Amurka dan magance matsalar tsaro

Najeriya na son siyo irin wadannan jiragen 12 daga kasar Amurka dan magance matsalar tsaro

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni sun ce gwamnatin tarayya na shirin siyo jiragen sama da ake kira da AH-1Z Viper attack helicopters guda 12 daga kasar Amurka. Shugaban sojojin sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ne ya wakilci Najeriya wajan zuwa kasar Amurka dan tattauna maganar siyen jiragen. Kakakin Hukumar sojin Saman Najeriya, Air Commodore Ehimen Ejodame ne ya fitar da sanarwar inda yace an yi ganawar tsakanin shugaban sojojin Najeriya da kuma wakilan kasar Amurka a birnin San Diego na jihar Califor...
Kotu ta daure abokai biyu da suka saci kayan sawa tsawon watanni 12 a gidan yari

Kotu ta daure abokai biyu da suka saci kayan sawa tsawon watanni 12 a gidan yari

Duk Labarai
Kotu a Jos, babban birnin jihar Filato ta yankewa abokai biyu hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari. Wadanda aka daure din sune, Michael Auta da Gabriel Sunday. Dukan su dai sun amsa laifinsu. Kayan da suka sata darajarsu ta kai Naira 488,000. Mai shari'a, Mrs Shawomi Bokkos ta yanke musu hukuncin daurin watanni 2 a gidan yari ko kuma su biya diyyar Naira 50000. Sannan ta bukaci kowannen su ya baiwa me shagon Naira 200,000 ko kuma a kara musu wani hukuncin daurin watanni 12. Dansanda me gabatar da kara, Insp Daniel Damulak ya gabatarwa da kotu cewa wata mata me suna Ms Gift Ernest ranar 17 ga watan Aprilu ya kai musu korafi. Ta yi zargin wadanda aka kama din sun shiga shagonta inda suka sace mata kayan da suka kai na Naira 488,000. Yace kuma bayan bincike duka sun...
Ana zargin “Gwamnan Gombe baya son Shugaba Tinubu yayi takara da Shettima a zaben 2027 saidai Tsoro ya hanashi fitowa ya fada”

Ana zargin “Gwamnan Gombe baya son Shugaba Tinubu yayi takara da Shettima a zaben 2027 saidai Tsoro ya hanashi fitowa ya fada”

Duk Labarai
Shiga tasharmu ta WhatsApp dan samun labarai: https://whatsapp.com/channel/0029VbA9rBN1SWt61nQZUj1g A yayin da ake dambarwa kan rade-radin canja mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima kamin zaben shekarar 2027. Rahotanni daga jaridar Vanguard na cewa, Wata majiya ta shaidawa jaridar cewa, Gwamnan Gombe, Inuwa Yahya baya son shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ci gaba da tafiya da Kashim Shettima a matsayin mataimaki musamman a zaben shekarar 2027. Saidai Gwamnan ya kasa fitowa ya fadi abinda ke zuciyarsa saboda tsoro. Bakan na zuwa ne bayan da aka tashi Baran-Baran a taron masu ruwa da tsaki na Arewa maso gabas saboda an kira sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu amma ba'a kira sunan Kashim Shettima ba. Ana zargin akwai yiyuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai canja ...
Ji yanda aka kama wani me shekaru 33 a jihar Yobe da ya zakkewa jaririya me watanni 9

Ji yanda aka kama wani me shekaru 33 a jihar Yobe da ya zakkewa jaririya me watanni 9

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Yobe sun kama wani mutum me shekaru 33 da ya zakkewa jaririya me watanni 9. An kamashi ne a Damboa dake Potiskum. Hukumar 'yansandan tace ta kama Ibrahim Shaibu Goni ne bayan samun bayanan sirri game da laifin nasa. Kakakin 'yansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim yace wanda ake zargin ya dauki jaririyar daga hannun mahaifiyartane inda ya je ya aikata wannan aika-aika, sannan an samu wasu abubuwa a jikin jaririyar da suka tabbatar da zargin da ake masa. Yace duka wanda ake zargi da wanda yayi aika-aikar an mikasu ga Asibiti dan gudanar da bincike inda yace kwamishinan 'yansandan jihar yayi Allah wadai da lamarin.
Nima ina tare da Kashim Shettima, inji Tauraron Kannywood, Shamu Dan Iya

Nima ina tare da Kashim Shettima, inji Tauraron Kannywood, Shamu Dan Iya

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Shamsu dan iya ya bayyana goyon bayansa ga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima. Hakan na zuwane bayan dambarwar data faru a wajan taron hadin masu ruwa da tsaki na jihohin Arewa Maso gabas inda aka samu hatsaniya bayan da me magana yace suna tare da Tinubu ba tare da kiran sunan kashim Shettima ba. Itama dai Tauraruwar fina-finan Hausa, Rahama Sadau tace tana tare da Kashim Shettima.
WATA SABUWA: Idan Ba Kashim Shettima Babu Ƙuri’un Arewa Maso Gabas Ga APC A 2027, Martanin Gwamna Zulum Ga Ganduje

WATA SABUWA: Idan Ba Kashim Shettima Babu Ƙuri’un Arewa Maso Gabas Ga APC A 2027, Martanin Gwamna Zulum Ga Ganduje

Duk Labarai
Idan Ba Kashim Shettima Babu Ƙuri'un Arewa Maso Gabas Ga APC A 2027, Martanin Gwamna Zulum Ga Ganduje. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"transform":1,"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Ma’anar wannan jawabi: Wannan kalami na nuni da cewa Shettima (Mataimakin Shugaban Kasa) na da matuƙar muhimmanci ga nasarar jam’iyyar APC a yankin Arewa maso Gabas. Gwamna Zulum yana jan kunne cewa idan aka watsar da Shettima ko aka cire shi daga tikitin takara a 2027, yankin ba zai marawa jam’iyyar baya ba. Dalilan wannan jawabi: Goyon ...
Bidiyo: Saboda Murna, Ji nayi kawai hawaye ya zubomin>>Inji Sheikh Zakzaky

Bidiyo: Saboda Murna, Ji nayi kawai hawaye ya zubomin>>Inji Sheikh Zakzaky

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Babban Malamin Shi'a, Sheikh Zakzaky ya bayyana cewa, saboda murna ji yayi kawai hawaye ya zubo masa. Zakzaky ya bayyana hakane a cikin wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda yake bayyana murna da martanin da Kasar Iran ta mayarwa da kasar Israyla. Yaki ya barke tsakanin kasar Israyla da Iran ne bayan da Israylan ta afkawa Iran da zummar cewa tana son hanata mallakar makamin kare dangi. https://www.tiktok.com/@abubakarj.labbaika/video/7...
‘Yan kasuwar man fetur sun kara kudin man a gidajen sayar da man fetur na Najeriya

‘Yan kasuwar man fetur sun kara kudin man a gidajen sayar da man fetur na Najeriya

Duk Labarai
A yayin da rikicin kasar Israyla da Falasdiynawa yasa farashin danyen man fetur a kasuwannin Duniya ya tashi zuwa dala $74 kan kowace ganga. 'Yan kasuwar man fetur a Najeriya sun kara farashin man fetur din nasu a gidajen mai daban-daban. Misali gidan man Aiteo ya kara farashin man fetur dinsa zuwa Naira 840 kan kowace lita daga Naira 835 da ake sayar da ita a baya. Hakanan gidan man Pinnacle sun kara farashin man fetur dinsu zuwa 845 akan kowace lita maimakon Naira 829 da suke sayarwa a baya. Dangote kuwa ya kara farashin man nasa ne zuwa Naira 840 kan kowacw lita maimakon 830 da yake sayarwa a baya. Ana tsammanin farashin man fetur din zai ci gaba da tashi a kasuwannin Duniya saboda rashin tabbas a kasuwar.