Thursday, March 26
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Atiku Abubakar ya bayyana cewa ba zai bar jam’iyyar PDP ba amma ya fadi dabarar da zasu yi amfani da ita dan kawar da Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Madugun Adawar Siyasa A Najeriya kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa yana nan daram a cikin jam’iyyar PDP, kuma ba shi da niyyar ficewa daga cikinta. Ya bayyana hakan ne a wata ganawa da mata mambobin Kwamitin Amintattu na jam’iyyar (BoT) da suka kai masa ziyara domin neman hanyoyin ceto jam’iyyar daga rushewa gaba daya. A cewar Atiku, rahotannin da ke cewa yana shirin barin PDP zuwa wata jam’iyya kamar SDP ba su da tushe balle makama, kuma an kirkire su ne domin rikita shirin kafa kawancen jam’iyyun adawa da ake yi. Ya jaddada cewa yana nan a matsayin cikakken memba na PDP, kuma yana jagorantar yunkurin kafa kawancen jam’iyyun adawa domin kalubalantar jam’iyyar APC a zaben 2027. A wata ganawa da aka yi a Abuja, Atiku y...
‘Yan Bìndìgà sun fi Sojojin Najeriya kayan aiki masu kyau>>Inji Majalisar tarayya

‘Yan Bìndìgà sun fi Sojojin Najeriya kayan aiki masu kyau>>Inji Majalisar tarayya

Duk Labarai
Majalisar wakilai ta bayyana cewa alamu na kara fitowa fili dake nuna mayakan Kungiyar Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau. Majalisar ta bayyana hakane a zamanta na ranar Talata inda ta bayyana damuwa matuka kan harin da ake zargin kungiyar ta Boko Hàràm da kaiwa a barikin sojoji ta Giwa dake jihar Borno. Majalisar tace wannan alamace karara dake nuna cewa mayakan kungiyar ta Bòkò Hàràm sun fi sojojin Najeriya makamai masu kyau. 'yan majalisar sun kuma bayyana damuwa kan yanda kungiyar ke dawowa a hankali da kuma asarar rayukan da ake samu a hare-haren da take kaiwa a jihohin Borno da Yobe. Duk da yawan kudin da gwamnati ke warewa bangaren tsaro na karuwa duk shekara, amma korafi na yawa a kan yawa ko ingancin makaman da ake siyowa sojojin. Misali a shekarar...

Bidiyo Da Duminsa: Kasar India ta Jefawa kasar Pakistan makami inda ya kàshè karamin yaro da jikkata mutane 2

Duk Labarai
Rahotanni daga Fakistan na cewa, Kasar India ta jefa mata makami inda ya kashe yaro ya jikkata mutane 2. Lamarin na zuwane yayin da ake tsaka da yakin cacar baki tsakanin kasashen biyu. Saidai da yawa sun ce India ta yi gaggawar kaiwa Pakistan harin. https://twitter.com/dom_lucre/status/1919866361804706171?t=9WDskLmZiFyzjkOqiS8Tng&s=19 https://twitter.com/dom_lucre/status/1919865357608657377?t=X9pQHu9qyQ6jZXiaEyintg&s=19 https://twitter.com/dom_lucre/status/1919867598478418263?t=EN9LXuWOYGic8JcsFFtojg&s=19 Wasu rahotanni dai sun ce Pakistan din ta sha Alwashin yin ramuwar gayya. Kasar ta Pakistan ta sanar da kulle sararin samaniyar ta na tsawon awanni 48 inda tace tana shirin kai harin ramuwar gayya. Tuni shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayy...
Arewa kadai ba zata iya sa dan takara ya ci shugaban kasa ba>>Tanko Yakasai

Arewa kadai ba zata iya sa dan takara ya ci shugaban kasa ba>>Tanko Yakasai

Duk Labarai
Babban dan siyasa daga jihar Kano, Alhaji Tanko Yakasai ya bayyana cewa, kuri'ar Arewa kadai ba zata saka dan takara ya ci zaben shugaban kasa ba. Yace hakanan kuri'ar kudu kadai itama ba zata sa mutum ya ci zaben shugaban kasa ba. Yace dole sai yankunan biyu sun hada kai sun kawo dan takara da ya ke da karbuwar da zata sa ya ci zabe, yace kuma dole dan takarar ya zamana yana da kudi. Yace saboda zaben Najeriya dole sai da kudi ake cinsa.
Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC

Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC

Duk Labarai
Ƴan Majalisar Wakilai 6 daga jihar Delta sun fice daga PDP zuwa APC Ƴan majalisar wakilai 6 daga jihar Delta sun sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC. Shugaban majalisar, Abbas Tajuddeen ne ya bayyana haka a zaman majalisar na yau Talata bayan ta dawo daga hutu. Yan majalisa shidan da su ka sauya sheka daga PDP zuwa APC sun hada da Victor Nwokolo; Dan majalisa Julius Pondi; Dan majalisa Thomas Ereyitomi; Nicholas Mutu; Okodiko Jonathan da kuma Nnamdi Ezechi. Wasu ‘yan jam’iyyar Labour ma guda biyu daga jihar Enugu su ma sun sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa ta PDP, waɗanda su ka hada da Mark Obetta da Dennis Nnamdi. Shugaban majalisar ya ambato ‘yan majalisar na cewa sun sauya sheka ne sakamakon rikicin da ya barke a jam’iyyunsu a jihohinsu da kuma a matakin ...
Nnàmdì Kanu ya karyata lauyan da ke kare shi ana tsaka da zaman kotu

Nnàmdì Kanu ya karyata lauyan da ke kare shi ana tsaka da zaman kotu

Duk Labarai
Nnamdi Kanu ya karyata lauyan da ke kare shi ana tsaka da zaman kotu An samu ɗambarwa a kotu ranar Talata yayin da shugaban haramtacciyar ƙungiyar, IPOB , Mazi Nnamdi Kanu, ya karyata wani lauya mai suna Charles Ude da ya bayyana kansa a matsayin wanda ke wakiltarsa. Kanu yana fuskantar tuhume-tuhume da suka shafi ta’addanci a gaban kotu. A lokacin zaman kotun, alkalin da ke jagorantar shari’ar ya jawo hankalin ɓangarorin da ke cikin shari’ar zuwa wata wasika daga Charles Ude, wanda ya ce shi ne lauya na gaskiya da ke kare wanda ake tuhuma. Sai dai tawagar lauyoyin da ke kare Kanu sun ce ba su san Ude ba, kuma Kanu da kansa ya tabbatar da hakan, yana mai jaddada cewa Agabi ne kawai lauyansa. Kotu ta kuma tabo batun yawan lauyoyin da ke wakiltar wanda ake tuhuma. A cew...
HOTO: Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya gana da shugaban ƙasa Bola Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin.

HOTO: Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya gana da shugaban ƙasa Bola Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin.

Duk Labarai
HOTO: Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya gana da shugaban ƙasa Bola Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Litinin. Wannan dai ita ce ziyarar aiki ta farko da ya kai wa shugaban ƙasar biyo bayan sauya sheka da ya yi zuwa jam’iyyar (APC). Gwamna Oborevwori ya isa gidan gwamnatin da misalin karfe 3:30 na rana. kuma manyan jami'ai ne suka tarbe su kafin su tafi ganawar sirri da shugaban.
Iyalan Mafarautan Da Aka Kàshè A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya

Iyalan Mafarautan Da Aka Kàshè A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya

Duk Labarai
Iyalan Mafarautan Da Aka Kashe A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya. Iyalan wasu mafarauta da suka rasa rayukansu a harin da ya faru a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga domin neman a biya su diyyar ‘yan uwansu da kuma gurfanar da wadanda suka aikata wannan mummunan laifi. Zanga-zangar, wadda ta gudana kwanaki 40 bayan aukuwar lamarin, ta samu halartar daruruwan ‘yan uwa da abokan arziki na wadanda abin ya shafa, wadanda suka fito dauke da takardu da hotunan wadanda suka mutu suna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su dauki matakin gaggawa. Wani daga cikin shugabannin iyalan, ya bayyana cewa:"Har yanzu ba a kama ko daya daga cikin wadanda suka aikata wannan kisa ba. Mun gaji da jiran shiru. Muna so a tabbatar mana da adalci kuma a tallafa mana da diyya domin wadanda suka bar...