Bankin First Bank ya kori manyan ma'aikatansa su 100.
An kori ma'aikatanne dga aiki saboda su bada guri a nada sabbin jini su shugabanci harkar bankin.
Hakan na zuwane bayan da babban dan kasuwa, Femi Otedola ya sayi hannun jari mafi yawa a bankin wanda ya koma karkashin kulawarsa.
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja sun bayyana cewa, An kama wani mutum da muggan makamai a birnin tarayyar.
Mutumin me suna, Obinna Nwigwe An kamashi ne bayan samun bayanan sirri daga Najob Guest House dake Bwari.
A yayin da jami'an tsaro suka je kamashi, an iskeshi ya harbi wani mutum bayan da suka yi gaddama.
Bincike da aka yi sosai a gidansa an gano karin makamai da Albarusai.
wanda ya harba din, Andrew Philemonna can Asibiti yana jinya, a yayin da shi kuma ake bincike akansa.
Ana zargin wani matashi da kashe mahaifiyarsa sannan ya jefa gawarta a cikin rijiya a Jihar Cross River.
Lamarin ya farune ranar Lahadi a titin Chairman Road, dake garin Ohong karashin karamar hukumar Obudu na jihar.
A wani bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook, an ga yanda mutanen unguwa suka taru ake zaro gawar matar daga rijiyar da dan nata ya jefata.
Rahotanni sunce wani abokinsa ne ya taimaka masa wajan gudanar da wannan danyen aikin.
Ya yiwa 'yar aikin gidansu baranar cewa idan ta sake ta gayawa wani sai ya kasheta.
Ya dauki yarinyar aikin gidan nasu akan mashin zuwa wani wajene inda akan hanya 'yan Bijilante suka taresu, anan ne Asirinsa ya tonu.
Babban fasto, Primate Ayodele ya bayyana abubuwan da zasu faru a shekarar 2025 kamar yanda ya saba yi duk shekara inda yake ikirarin an masa wahayi.
Faston yace wasu daga cikin abubuwan da aka masa wahayi shine cewa za'a saki shugaban kungiyar IPOB dake son kafa kasar Biafra watau, Nnamdi Kanu, sannan matsin rayuwa zai karu a shekarar ta 2025.
Yace ya kuma gano cewa wani gwamna zai mutu, sannan za'a yi yunkurin kashe wani shugaban kasa ta hanyar zuba masa guba amma zai tsallake, saidai be bayyana kowane shugaban kasa bane.
Ya kuma za'a samu matsalar kisan jami'an tsaro na FBI da CIA na kasar Amurka.
Bayan Amarya Ta Gudu A Safiyar Ranar Daurin Aurensu, A Karshe Ango Ya Auri Daya Daga Cikin Kawayen Amarya A Ranar Auren
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya auku ne a garin Sabo-Ibadan dake jihar Oyo.
Me za ku ce?
A Yanzu Haka Za A Iya Biyan Naira Dubu Talatin A Matsayin Sadaki, Inji Limamin Masallacin Albabello Dake Zaria
Malamin ya ce "kamar yadda ya tabbata a mazhabar Imam Malik za a iya biyan rub'u dinar ko darhami uku, inda dubu talatin ce kiyasin darhami uku", Inji- Imam Dr. Hamza Assudaniy Babban Limamin Masallacin Juma'a Na Albabello Zaria.
Da Mu Da Kwankwaso Duk Tinubu Muka Yi Wa Aiki A Zaben 2023, Kuma Idan Har Kwankwason Da Na Sani Ne Zai Sake Sabunta Wannan Kwangilar A 2027, Inji Dan Bilki Kwamanda
Me za ku ce?
Wani rahoto da ya bayyana, ya nuna shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaba Mafi rashawa da cin hanci inda ya zo a matsayi na 3 a Duniya.
Wata kungiya me suna, (OCCRP) ce ta bayyana hakan.
Ta kuma samu wanna sakamako ne bayan da ta nemi a yi zabe dan fitar da mutane mafiya rashawa a Duniya.
Kungiyar ta hada da manyan 'yan Jarida ne da 'yan fafutuka dan kare hakkin al'umma. Shugban kasar Kenya, William Ruto ne ya zo na daya sai kuma shugaban kasar Indonesia, Joko Widodo ya zo na uku.
Hambararren Shugaban kasar Syria, Bashar al-Assad ne ya zamo gwarzon shekara.
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, bai yi wata murna da zama shugaban kasa ba bayan da ya iske irin barnar da aka yiwa Najeriya.
A bayyana hakane ga kakakin majalisar dattijai, Godwill Akpabio.
Akpabio ne ya bayyana hakan a wajan rabon kayan da yayi ga mutanen mazabarsa wanda suka hada da kayan abinci da ababen hawa da sauransu a jiharsa ta Akwa-Ibom.
Yace wata rana ya taba tabayar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan shin ko yayi murnar zama shugaban kasa kuwa lura da irin barnar da ya iske tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele yawa kasar?
Sai shugaba Tinubu yace masa murna kadan yayi. Bai san barnar da akawa Najeriya ta kai haka ba.
Akpabio ya kara da cewa, ya gayawa shugaban kasar cewa, yayi imanin kamar yanda ya gyara Legas, Itama Na...
Bincike ya nuna cewa, matasa dake tsakanin shekaru 21 zuwa 30 ne a Najeriya suka fi amfani da maganin karfin maza .
Yawanci ana sayen magungunan kara karfin maza ne dan samun kuzari da jin dadin jima'i.
Saidai da yawa daga cikin magungunan da ake sayarwa din basu da rijista hukukomin lafiya na kasa basu tantance su ba, hakanan kuma mafi yawan masu sayar da magungunan ma basu da ilimi akan harkar maganin.
Hakan yasa ake samun matsalar magungunan su rika bayar da illa ga lafiyar dan adam inda akan samu matsalar mazaje na mutuwa yayin jima'i.