Tuesday, April 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bamu hada kai da kowace Jam’iyya ba kan maganar 2027>>Peter Obi

Bamu hada kai da kowace Jam’iyya ba kan maganar 2027>>Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na Jam'iyyar Labour Party a shekarar 2023, Peter Obi ya bayyana cewa babu wata yarjejeniyar hadaka da aka cimma tsakaninsa da wata jam'iyyar Adawa. Peter Obi ya bayyana hakanne a Abuja yayin ganawa da manema labarai. Saidai bai karyata cewa akwai tattaunawa da ake tsakaninsa da jam'iyyun Adawa ba amma yace ba'a cimma yarjejeniya ba. Peter Obi ya bayyana cewa akwai bukatar samun hadin kai tsakanin 'yan Najeriya ba tare da la'akari da banbancin Jam'iyya ba inda yace ta hakane kadai za'a samu nasarar kwace mulki daga hannun APC dake mulkin kama karya a Najeriya. Ya bayyana damuwa kan cewa 'yan Najeriya da yawa bmna bakuntar Lahira basu shirya ba saboda matsalolin tsaro da gwamnati ta kasa shawo kansu
Gwamnatin tarayya zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da matatar man fetur ta Dangote

Gwamnatin tarayya zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da matatar man fetur ta Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya na shirin rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa da kamfanin matatar man Dangote. Hakan na zuwane bayan da matatun man fetur na Gwamnati, na Fatakwal dana Warri suna dawo suka ci gaba da aiki. Rahoton jaridar Punchng ya ruwaito cewa dan samarwa wadannan matatun man fetur na gwamnati isashshen danyen man fetur din, Gwamnatin zata rage yawan danyen man fetur din da take sayarwa matatar man fetur ta Dangote. Hakan, a cewar masana tattalin Arziki, zai sa a samu gasa sosai a kasuwar man fetur din wanda hakan zai yi sanadiyyarf faduwar farashin man fetue din.
A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura

A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura

Duk Labarai
A FADA A CIKA: Sheik Pantami Ya Gwangwaje Wasu Abokan Karatunsa Na Sakandire Da Babura. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Shehin Malamin ya bada baburan ne bayan alkawarin da ya yi musu a yayin da suke taron tsoffin dalibai.
Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina

Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina

Duk Labarai
Wasu Daga Cikin Kayayyakin Da Rundunar 'Yan Sandan Jihar Katsina Ta Kama Hannun Masu Aikata Laifuka Daban-daban Katsina. A Karkashin Jagorancin Kwamishinan Yansanda, Aliyu Abubakar Musa A Cikin Shekarar Da Ta Gabata, Wanda Jami'in Hulda Da Jama'a Na Rundunar Yan Sandan Jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu Ya Baje-kolin Su Yau Alhamis. Daga Jamilu Dabawa, Katsina
Matafiya na shan wuyar sayen tikitin jirgin kasan Abuja-Kaduna ta intanet

Matafiya na shan wuyar sayen tikitin jirgin kasan Abuja-Kaduna ta intanet

Duk Labarai
Duk da shigo da tsarin sayan tikitin shiga jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ta intanet da gwamnatin Najeriya ta yi a shekarar 2021, har yanzu fasinjoji na shan dan karen wuya kafin samun shi. Tsohon ministan sufurin kasar Rotimi Amaechi ne ya fito da tsarin a zamanin mulkin tsohon shugaban kasar Muhammadu Buhari, da nufin magance cuwa-cuwar saida tikitin da ake zargin ma'aikatan wurin na yi. Gwamnatin Najeriya ta kashe naira miliyan 900 domin inganta hakan, sai dai bincike na baya-bayan nan da jaridar Solacebase ta fitar, ta raiwato a tashar jirgi ta Idu da Kubuwa a Abuja babban birnin kasar ya nuna bata sauya zani ba. Dubban matafiyan da a kowacce rana suka dogara da jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna na shan dan karen wuya kafin samun tikitin, ko dai dalilin rashinsa a intanet...
Najeriya ta ware biliyan 60 na ciyar da ƴan firamare a 2025

Najeriya ta ware biliyan 60 na ciyar da ƴan firamare a 2025

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ware naira biliyan 60 domin ciyar da 'yan makarantar firamare a sassa daban-daban na kasar a cikin kasafin kudin 2025. Za ai aikin ne karkashin shirin gwamnati na farfado da tattalin arziki wato Economic Recovery Growth Plan (ERGP). Jaraidar Dailty Trust ta tawaito cewa, kafin a sauya ministan ilimin kasar ya fara sanar da hakan wanda dama shirin ciyar da daliban yake karkashin ma'aikatarsa, kafin daga bisani a mayar da shi karkashin ofishin shugaban kasa. An ware wa ma'aikatar ilimi kudi naira biliyan 348, cikin sama da naira tiriliyan 2. 517, wanda hakan na daga cikin fannin da ya fi samun kaso mai tsoka a kasafin kudin, duk da bai kai adadin da Bankin Duniya ya bayar da shawara na kashi 20 zuwa 30 cikin 100 na kasafin kudin ba. Har wa yau, ma'aikatar il...
An kuɓutar da wani yaro bayan kwana biyar tare da zakuna da giwaye

An kuɓutar da wani yaro bayan kwana biyar tare da zakuna da giwaye

Duk Labarai
An kuɓutar da wani yaro ɗan shekara takwas, bayan shafe kwana biyar a gandun dajin zakuna da giwaye a arewacin ƙasar Zimbabwe. Lamarin ya faru ne a lokacin da yaron mai suna Tinotenda Pudu ya yi ta gararamba a cikin gandun daji Matusadona Game Park, kamar yadda ɗan majalisar gabashin yankin Mashonaland, mai suna Mutsa Murombedzi ya kuma wallafa a shafinsa na X. Kwanan sa biyar a dajin yana bacci kan duwatsu, ga kuma gurnanin zakuna da wucewar giwaye, babu abin da ya ke ci sai 'ya'yan itatuwa. Gandun dajin Matusadona dai na ɗauke da zakuna 40, akwai lokacin da ya kasance wuri mafi yawan zakuna a Afirka, kamar yadda bayanan African Parks suka bayyana.
Ɗansanda ya sha barasa ya saki mutum 13 da ke tsare

Ɗansanda ya sha barasa ya saki mutum 13 da ke tsare

Duk Labarai
Wani jami'in ɗansanda da ya yi mankas da barasa a Zambiya ya saki wasu mutum 13 da ke tsare a ofishin 'yansanda domin su je su yi shagalin murnar sabuwar shekara. Jami'ai sun ce an kama sufeto Titus Phiri bayan sakin mutanen da ake tsare da su a wani ofishin 'yansanda a Lusaka, babban birnin ƙasar. Mutane 13 da ya saki, ana zarginsu da aikata manyan laifuka da suka haɗa da kisan kai da fashi. Yanzu haka mutanen sun tsere, kuma tuni aka ƙaddamar da farautarsu.