Monday, April 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Karanta Jadawalin Alkawuran da Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wanda bata cikasu ba a shekarar 2024

Karanta Jadawalin Alkawuran da Gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi wanda bata cikasu ba a shekarar 2024

Duk Labarai
A yayin da ya rage saura kwanaki kadan mu shiga shekarar 2024, mun kawo muku jadawalin alkawuran da Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi wadanda bata cikasu ba a wannan shekarar. Alkawarin cire haraji akan kayan Abinci Cire Haraji akan kayan Abinci dan samarwa talakawa hanyar saukin rayuwa abune da gwamatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta alkawarta ta bakin Ministan Noma, Abubakar Kyari. Yace za'a cire haraji akan Alkama, Shinkafa, Masara da sauransu dan samarwa mutane saukin rayuwa. A ranar 14 ga watan Augusta, Hukumar Kwastam ta sanar da izinin data samu daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dan cire tallafin. Hukumar kwastam tace cire harajin zai fara aiki ne daga 15 ga watan July zuwa 15 ga watan Disamba. Saidai da ba'a ga an cire harajin ba, an ...
Sojoji Sun Yi Sìĺaŕ Mutuwar Mutanen Da Ba Su Ji Ba, Ba Šu Ģàñi Ba Tare Da Àsarar Dabbobi Da Gidaje Da Dama A Bisa Kuskure, A Yayin Kai Farmaki A Kauyen Gidan Bisa Da Runtuwa Dake Karamar Hukumar Silame Dake Jihar Sokoto

Sojoji Sun Yi Sìĺaŕ Mutuwar Mutanen Da Ba Su Ji Ba, Ba Šu Ģàñi Ba Tare Da Àsarar Dabbobi Da Gidaje Da Dama A Bisa Kuskure, A Yayin Kai Farmaki A Kauyen Gidan Bisa Da Runtuwa Dake Karamar Hukumar Silame Dake Jihar Sokoto

Duk Labarai
INNANILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Sojoji Sun Yi Sìĺaŕ Mutuwar Mutanen Da Ba Su Ji Ba, Ba Šu Ģàñi Ba Tare Da Àsarar Dabbobi Da Gidaje Da Dama A Bisa Kuskure, A Yayin Kai Farmaki A Kauyen Gidan Bisa Da Runtuwa Dake Karamar Hukumar Silame Dake Jihar Sokoto. Muna rokon Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu. Daga Real Buroshi Mawaka Sokoto
Kungiyar B0k0 Hârăm sun kai hari a sansanin sojojin Najaria dake Borno da jirgi marar matuki

Kungiyar B0k0 Hârăm sun kai hari a sansanin sojojin Najaria dake Borno da jirgi marar matuki

Duk Labarai
A kalla Sojoji 6 ne suka jikkata biyo bayan harin da aka kai wa sansaninsu dake Jihar Borno da jirgi marar matuki wanda ake zargin Kungiyar B0k0 Hàràm da kaiwa. An kai harinne a Wajiroko dake karamar Hukumar Damboa da yammacin ranar Talata. Waji soja da ya shaida lamarin ya gayawa majiyar Hutudole.com cewa da farko sun ji kamar karar jirgin sama inda daga baya suka ji karan fashewar abubuwa. Hutudole.com ya fahimci cewa, a baya Kungiyar ta B0K0 Hàràm ta taba kai hari kan sansanin inda suka yi harbin kan mai uwa da wabi wanda daga baya sojojin suka dakile harin. Wata majiya tace an lalata motar yaki ta sojoji guda 1 a yayin harin.
Hirar da ‘yan Jarida suka yi da Shugaba Tinubu ta nuna bai damu da halin da mutane ke ciki ba>>Inji PDP

Hirar da ‘yan Jarida suka yi da Shugaba Tinubu ta nuna bai damu da halin da mutane ke ciki ba>>Inji PDP

labaran tinubu ayau
Jam'iyyar hamayya ta PDP ta bayyana cewa, hirar da 'yan Jarida suka yi da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta farko tun bayan hawansa mulki a Ranar Litinin ta nuna cewa bai damu da halin da 'yan Najeriya ke ciki ba. Me magana da yawun PDP, Debo Ologunagba ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar inda yace maganar da shugaban kasar yayi ta cewa bai yi nadamar cire tallafin man fetur ba ta nuna bai damu da halin da mutane ke ciki ba. Yace shugaban kasar kamata yayi ya nuna damuwa akan halin da mutane ke ciki da kuma bayyana hanyoyin da zasu dauka dan kawowa mutane sauki. Yace ba gaskiya bane maganar shugaban kasar ta cewa an samu ci gaba a kasarnan bayan hawan mulkinsa, inda yace mutuwar da aka rika yi wajan turmutsutsu na karbar abincin tallafi alamace dake nuna irin halin kun...
Ba’a kwace min Fili a Abuja ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari

Ba’a kwace min Fili a Abuja ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya musanta rahotannin dake yawo cewa, wai an kwace masa fili a babban birnin tarayya, Abuja. Buhari ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Malam Garba Shehu Inda yace shugaba Buharin Nada fili a Abuja amma ba'a kwaceshi ba. Yace filin da ake magana akai na wata gidauniya ce da aka sawa sunan tsohon shugaban kasar kuma ba mallakin tsohon shugaban kasar bace. Yace hukumar kula da filaye ta Abuja da gangan ta tsawwala kudi ga masu gidauniyar a yayin da suka je Neman shaidar mallakar filin watau CofO. Yace koda a lokacin da Buhari ke shugaban kasa an kawo fom wanda zai cike a bashi fili a Abuja amma yace baya so Dan yana da filin.