Ji yanda Gwamnan jihar Kebbi ya bayyana cewa DSS sun gargadesu game da yunkurin dauke daliban makarantar ‘yanmata ta MAGA, kuma sun kai jami’an tsaro amma Mintuna 30 kamin tshageran daji su kwashe daliban sai jami’an tsaron suka bar makarantar
Rahotanni na fitowa cewa hukumar 'yansandan Farin kaya ta DSS yi gargadin cewa ana shirin kai wa makarantar 'yan mata ta MAGA dake jihar Kebbi hari.
Gwamman jihar Kebbi, Mohammed Nasir Idris ya tabbatar da cewa DSS sun sanar dasu game da gargadin kuma suka bayar da shawarar a gudanar da taron tsaro kan lamarin.
Gwamnan yace sun gudanar da taro akan tsaro aka kai jami'an tsaro makarantar dan su tsare daliban amma sai suka buge da daukar hotuna da dalibai 'yan mata 'yan makarantar.
Gwamnan yace mintuna 30 kamin a kai harin, jami'an tsaron dake baiwa makarantar kariya sun janye suka kama gabansu.
Gwamnan ya kai ziyara makarantar ranar Litinin da misalin karfe 6:45 na safe kamar yanda kafar Pointblacknews.com ya ruwaito.
Kafar tace wani jami'in tsaro ya bayyana mata cewa, gwamna...








