Wednesday, February 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Wannan Bidiyon daya nuna cikin Cell din ‘yansandan Najeriya da yanda ake tsare da masu laifi ya dauki hankula

Wannan Bidiyon daya nuna cikin Cell din ‘yansandan Najeriya da yanda ake tsare da masu laifi ya dauki hankula

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya nuna cikin Cell din 'Yansandan Najeriya da kuma yanda ake tsare da masu Laifi. A Bidiyon an ga wani me laifi ko wanda ake zargine yake daukar Bidiyon da wayarsa. Da yawa sun rika tambayar shin dama ana barin masu laifi su shiga dakin da ake tsaresu da waya? Sannan wasu sun rika tambayar shin a ina suke fitsari da kashi, saboda ba'a ga bayi ba. https://twitter.com/dammiedammie35/status/2004419462175641904?t=luWLt-zwLg-MYVTRObmuKQ&s=19
Gwamnatin Najeriya karya take, Amurka bata sanar da ita Khàrìn data kai sokoto ba>>Inji Omoyele Sowore

Gwamnatin Najeriya karya take, Amurka bata sanar da ita Khàrìn data kai sokoto ba>>Inji Omoyele Sowore

Duk Labarai
Mawallafin Jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya karya take Amurka bata sanar da ita ba kamin ka harin Sokoto. A safiyar yau ne dai aka tashi da rahoton cewa, Kasar Amurka ta kai hari Kan wanda ta zarga da yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi. Sowore dai yace wannan abin kunyane ace kasa Kamar Najeriya ta koma 'yar kallo wajan magance matsalar tsaronta sai an zo an taimaka mata. Sowore yace Idan aka samu shugabanci na gari, Najeriya zata samu tsaro. https://twitter.com/sowore/status/2004387413045698672?t=uGvRbzeYTl6XqqMvdJ7ByA&s=19
Gwammatin Najeriya ta amince mana kamin Khàrìn da muka kai Sokoto>>Inji Kasar Amurka

Gwammatin Najeriya ta amince mana kamin Khàrìn da muka kai Sokoto>>Inji Kasar Amurka

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta amince mata kamin harin da ta kai jihar Sokoto. Shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar da kai harin inda yace sun kai harinne me hatsarin gaske kan masu yiwa Kiristoci Khìsàn Kyìyàshì Yace yayi gargadi a baya ba'a jishi ba amma yanzu jiki Magayi Ya bayyana cewa, kuma idan Kyìsàn Kiristocin ya ci gaba, zasu sake kawo harin.
Kalli Hotunan: Mohammed Salah ya wallafa Kwalliyar Kirsimeti kamar yanda ya saba duk da yana musulmi

Kalli Hotunan: Mohammed Salah ya wallafa Kwalliyar Kirsimeti kamar yanda ya saba duk da yana musulmi

Duk Labarai
Tauraron dan kwallon Liverpool, Mohammed Salah kenan a wadannan hotunan inda yake nuna Kwalliyar Kirsimeti. An ga 'ya'yansa a cikin Kwalliyar kirsimeti suna sanye da jajayen kaya, lamarin ya jawo cece-kuce musamman ganin cewa yana musulmi yace hakan https://twitter.com/MoSalah/status/2004227703009116375?t=paz4UAN3GcwvzMbtdtm53w&s=19
Kalli Bidiyon: Kailani Muhammad wanda yayi zargin Kudin Dangote ba na halal bane, ya fito ya baiwa Dangoten hakuri

Kalli Bidiyon: Kailani Muhammad wanda yayi zargin Kudin Dangote ba na halal bane, ya fito ya baiwa Dangoten hakuri

Duk Labarai
Kailani Muhammad wanda ya fito ya bayyana rashin jin dadi game da abinda Dangote yawa Farouk Ahmed sannan yace shi Dangoten ma ya kamata ya fito ya gaya musu yanda ya samu kudinsa a Fatakwal. Saidai Maganar batawa Dangote dadi ba inda ya fito yace Kailani Muhammad ya fito ya janye kalamansa sannan ya bashi hakuri idan ba haka ba zai makashi a kotu ya nemi ya biyashi diyyar Biliyan 100. Hakan yasa Kailani Muhammad ya fito ya janye kalaman nasa tare da baiwa Dangoten hakuri. https://twitter.com/Minikothe3rd/status/2003913417082785886?t=Yifue42xllwHQcfnnOJccw&s=19
Tawagar ‘yan Kwallon Najeriya ta Super Eagles ne kadai basu je da masu goyon bayansu gasar cin kofin Africa ta AFCON ba a hukumance

Tawagar ‘yan Kwallon Najeriya ta Super Eagles ne kadai basu je da masu goyon bayansu gasar cin kofin Africa ta AFCON ba a hukumance

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Tawagar 'yan kwallon Najeriya ne kadai basu je gasar cin kofin AFCON dake wakana yanzu haka ba a kasar Morocco da tawagar masu goyon bayansu ba a hukumance. Rahotanni sun ce hukumomin kwallon kafar Najeriya sun ki zuwa da tawagar masu goyon bayan da aka saba zuwa dasu ne saboda wai babu kudi.
Kalli Bidiyon: Yanda wani dan siyasa ya sha da kyar a hannun Talakawa a jihar Kaduna

Kalli Bidiyon: Yanda wani dan siyasa ya sha da kyar a hannun Talakawa a jihar Kaduna

Duk Labarai
Wani dan siyasa ya sha da kyar a hannun Talakawa a jihar Kaduna. A Bidiyon da aka ga yana ta yawo a kafafen sadarwa, an ga mutane ma ta jifarsa suna fadar cewa bama yi. https://twitter.com/ADCVanguard_/status/2004159712368251018?t=QM4sH0Ih2PxAaO7ahRwQ5A&s=19 A makon da ya gabata dai Hutudole ya kawo muku Rahoton yanda kusan irin haka ta faru a jihar Zamfara inda acan ma wani dan siyasa ne ya sha da kyar.