Sunday, January 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Wannan Cin Amana har Ina: Ji Abinda Magidanci yayi bayan kama yaron dake masa aiki yana aikata Alfàshà da matarsa

Wannan Cin Amana har Ina: Ji Abinda Magidanci yayi bayan kama yaron dake masa aiki yana aikata Alfàshà da matarsa

Duk Labarai
Wani magidanci a Legas dake unguwar Victoria Garden City ya hallakà yaron aikin gidansa bayan kamashi yana aikata Alfasha da matarsa. Yaron aikin dan kimanin shekaru 20 sunansa Nengak kuma dan asalin jihar Filato ne wanda aka daukeshi aiki a gidan yana kai yara makaranta da aiken cefane da sauransu. Me gidan ya fara jin rade-radin cewa yaron na lalata da matarsa. Dalilin haka ya saka kyamarar CCTV kuma ya kamasu turmi da tabarya. Anan ya gayyato yaran layi sukawa yaron aikin gidan nasa duka har ya mutu. Abokin mamacin Bitrus Idi ne ya bayyana haka ga kafar Daily Post inda yace gawar sa na mutuware an ki basu inda 'yansanda suka ce sai sun biya kudi an yi bincike kan dalilin mutuwar tasa.
Kalli Bidiyon: Yanda aka Zargi wata Fastuwa da sayar da mai wanda tace duk wanda yayi amfani dashi yana hana Tshàgyèràn Dhàjì su sàcè mutum

Kalli Bidiyon: Yanda aka Zargi wata Fastuwa da sayar da mai wanda tace duk wanda yayi amfani dashi yana hana Tshàgyèràn Dhàjì su sàcè mutum

Duk Labarai
Wannan Fastuwar ta dauki hankula bayan da aka zargeta da sayar da wani mai Wanda tace duk wanda yayi amfani dashi, 'yan Bindiga ba zasu yi garkuwa dashi ba. An ganta tana karbar kudi tana bayar da man a cocinta. Lamarin dai ya jawo cece-kuce inda da yawa ke cewa akwai salon damfara a lamarin. https://twitter.com/ObaOfVibes/status/1997670841652334788?t=_toe3S-gGnnSVc3HL2aXzA&s=19
Kalli Bidiyon yanda wasu matasa suka Hàllàqà wani shugaban Fulani a jihar Benue, Sojoji sun kama wanda ake zargi suka damkawa ‘yansanda

Kalli Bidiyon yanda wasu matasa suka Hàllàqà wani shugaban Fulani a jihar Benue, Sojoji sun kama wanda ake zargi suka damkawa ‘yansanda

Duk Labarai
Rahotanni daga Ogbobia, dake jihar Benue na cewa, wasu matasa sun yiwa wani shugaban Fulani Kwantan Bauna suka hallaqashi. Sun bai wannan aika-aika ne yayin da yake kan hanyar zuwa garken shanunsa, hakanan sun bi garken shanun suka kashe su sannan suka sace wasu. Wani dake tare da shugaban Fulanin da ya samu kubuta daga hannun maharan ya garzaya gida ya fada, fulanin sun je suka gayawa wasu sojoji dake wajen. Ko da sojojin suka je wajan sun tarar da muharan akan gawar shugaban fulanin. Suna ganin sojojin sai suka tsere. Sojojin dai sun bisu inda suka kama guda daya suka mikashi hannun 'yansanda. Saidai Fulanin sun ce daga baya sun samu labarin 'yansandan sun sakeshi. shahararren dan fafutuka, VDM ne ya bayyana hakan inda ya wallafa hotunan yanda lamarin ya faru, yace f...
Yanzu-Yanzu: Bayan aiko da wakilanta suka ganewa idanunsu abinda ke faruwa a Najeriya, kasar Amurka tace lallai gaba dayan ‘yan Najeriya ne ya kamata a samarwa da tsaro

Yanzu-Yanzu: Bayan aiko da wakilanta suka ganewa idanunsu abinda ke faruwa a Najeriya, kasar Amurka tace lallai gaba dayan ‘yan Najeriya ne ya kamata a samarwa da tsaro

Duk Labarai
Dan majalisar kasar Amurka, Riley Moore wanda Shugaban kasar, Donald Trump ya wakilta ya zo Najeriya yaga yanda ake Mhuzghunawa Kiristoci kamar yanda suke zargi. Bayan ziyarar tasa yace a yanzu 'yan Najeriya gaba daya ne ya kamata a samarwa da tsaro. Saidai yace duk da haka sun fi damuwa da samarwa Kiristoci tsaro. Yace ya ji dadin yanda Najeriya ta amince zata yi aiki da kasar Amurka dan samarwa kasar tsaro amma ba a baki kawai abin ya kamata ya kasance ba. Kamata yayi a tabbatar da abubuwan da aka tattauna a aikace.
Kalli Bidiyon Da Duminsa:Yanda Matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta kùnyàtà gwamnan jihar Osun yayin da yake tsaka da jawabi tace ta bashi minti 5 ya gama jawabin da yake ya wuce ya ishesu

Kalli Bidiyon Da Duminsa:Yanda Matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta kùnyàtà gwamnan jihar Osun yayin da yake tsaka da jawabi tace ta bashi minti 5 ya gama jawabin da yake ya wuce ya ishesu

Duk Labarai
Matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta kunyata Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke yayin da yake jawabi a wajan taro. Ta taso ta sameshi tace ta gaggauta ya kammala jawabinsa ta bashi mintuna 5 ya ishesu da wake-wake. An ga ta gaya masa hakan cikin bacin rai tana nuna masa yatsa, kamar danta. Bidiyon dai ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa bai kamata tawa gwamna guda haka ba. https://twitter.com/thecableng/status/1998006035177406678?t=_0Vf3_gJVlfosVozjPLY6g&s=19
Abin Takaici ne Yàqìn Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno yafi Yàqìn Basasa na Najeriya dadewa>>Inji Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Abin Takaici ne Yàqìn Tshàgyèràn Dhàjì na jihar Borno yafi Yàqìn Basasa na Najeriya dadewa>>Inji Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana rashin jin dadinsa kan yanda yace yakin Bòkò Hàràm ya fi Yakin Basasar Najeriya dadewa. Yace yakin basasa ya dauki watanni 30 ana yinsa duk da sun yi tsammanin ba zai wuce watanni 6 ana yi ba, yace amma gashi yakin Bòkò Hàràm yanzu ya kai Najeriya Shekaru 15 ana yinsa. Yace ya je jihar Borno dan binciken dalilin Kafuwar Kungiyar inda yace ya samu cewa an so a yi sulhu dasu suka kiya amma daga baya suka yadda saidai sulhun ya ruguje bayan da gwamnati ta kasa ganawa da shuwagabanninsu.
Kalli Bidiyon: Tauraron Fina-finan Hausa, Shalele na shan Allah wadai saboda yanda aka ganshi da wata Budurwa kirjinta na tabashi manne a jikinta

Kalli Bidiyon: Tauraron Fina-finan Hausa, Shalele na shan Allah wadai saboda yanda aka ganshi da wata Budurwa kirjinta na tabashi manne a jikinta

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Shalele na shan suka da Allah wadai bayan da wani Bidiyonsa tare da wata da aka ganshi manne a jikinta korjinta na tabashi. Bidiyon dai wasu sun rika tsokanarsa wasu kuwa cewa suka yi bai kyauta ba. https://www.tiktok.com/@yardaraja0/video/7580545561699290375?_t=ZS-923FqC2nP0L&_r=1 Cikin wanda suka ce bai kyauta ba hadda abokin aikinsa, Garzali Miko wanda yace irin abinda Shalele ke yi ne ke jawo musu zagi. https://www.tiktok.com/@garzalimiko/video/7581140114294787348?_t=ZS-923GkPxA8Th&_r=1
Kalli Bidiyon yanda sojojin kasar Benin Republic suka yi yunkurin kàkkalàbò Jiragen sojojin saman Najeriya da suka shiga kasar dan hanasu yin Jhuyin mulki

Kalli Bidiyon yanda sojojin kasar Benin Republic suka yi yunkurin kàkkalàbò Jiragen sojojin saman Najeriya da suka shiga kasar dan hanasu yin Jhuyin mulki

Duk Labarai
Bidiyo ya bayyana yansa Jiragen yaki na Najeriya suka shiga kasar Benin Republic inda suka taimaka aka dakile yunkurin juyin mulki a kasar. Saidai Sojojin na kasar Benin Republic sun yi yinkirin kakkabo jiragen yakin Najeriya amma basu yi nasara ba. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1997925658689765818?t=Kvy0jTVe3y0KipsWgedHUw&s=19 https://twitter.com/BrantPhilip_/status/1997972722597429503?t=Q1T_cWjaaEG_9uKv0sSzdw&s=19
Bafulatani ya dauki hankula bayan da yayi korafin cin zalin da ‘yan Bijilante suka masa

Bafulatani ya dauki hankula bayan da yayi korafin cin zalin da ‘yan Bijilante suka masa

Duk Labarai
Wannan Bafulatanin ya dauki hankula bayan da ya bayyana irin cin zalin da 'yan Bijilante suka masa. Ya bayyana cewa ya siyo sabon mashin, shine 'yan Bijilante suka tareshi akan hanyar komawa gida suka ce sai ya basu dubu 10. Shi kuma yaki amincewa shine suka masa dukan kawo wuka suka kwace masa kudi dubu 40 da Power bank. Yace sai da aka kwantar dashi a asibiti. Ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tiktok. https://www.tiktok.com/@auren.ja.ri/video/7580761116498758930?_t=ZS-923D5BZiVcm&_r=1