Sunday, February 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

An gano gwamnatin Tinubu na biyan Tallafin man fetur ta bayan fage duk da ikirarin da take na cewa ta cire tallafin

An gano gwamnatin Tinubu na biyan Tallafin man fetur ta bayan fage duk da ikirarin da take na cewa ta cire tallafin

Siyasa
Wani sabon rahoto da jaridar Punch ta yi ya bayyana cewa, Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na biyan Tallafin man fetur. Hakanan akwai tanadin biyan tallafin ma har na Naira Biliyan 5.4 da za'a biya nan da karshen shekarar da muke ciki. Hakan na kunshene a cikin wani daftarin kokarin fitar da Najeriya daga matsin tattalin arzikin da take fama dashi. Daftarin ya kunshi baiwa mutane da yawa 'yan Najeriya kudin tallafi da kuma kawo saukin farashin kayan masarufi da sauransu. Rahoton yace gwamnati ta kasa cire tallafin man fetur din gaba daya lura da yanda a yanzu haka ake tsaka da matsin tattalin arziki me tsanani. Wannan daftari za'a yi amfani dashi ne cikin watanni 6 masu zuwa. Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu dai ta na ta ikirarin cewa ta cire tallafin man fetur amma...
Da Duminsa: Majalisar Jihar Kaduna ta bukaci a kama da hukunta tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai saboda zargin lalata kudin jihar har Naira Biliyan 423

Da Duminsa: Majalisar Jihar Kaduna ta bukaci a kama da hukunta tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai saboda zargin lalata kudin jihar har Naira Biliyan 423

Siyasa
Majalisar jihar Kaduna ta nemi a kama da hukunta tsohon gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da mukarrabansa saboda zargin lalata kudin jihar har Naira Biliyan 423. Kwamiti na musamman da aka nada yayi binciken mulkin tsohon gwamnan bisa jagorancin dan majalisa Henry Zacharia ya kammala binciken da mikawa majalisar sakamakon abinda ya gani. Kakakin majalisar, Yusuf Liman ya bayyana damuwa kan yanda yace ake zargin tsohon gwamnan da lalata Naira Biliyan 423. Sannan ana zargin El-Rufai da kuma bayar da kwagila ba bisa ka'ida ba da satar dukiyar jama'a da kuma aikata ba daidai ba. Rahoton kuma yace mafi yawancin kudaden da gwamnatin jihar ta ciwo bashi, ba'a yi amfani dasu yanda ya kamata ba.
Da ka zama talaka dake ta mazakuta, gara ka zama me kudin da be da mazakuta>>Sanata Shehu Sani

Da ka zama talaka dake ta mazakuta, gara ka zama me kudin da be da mazakuta>>Sanata Shehu Sani

Nishadi, Shehu Sani, Siyasa
Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa, da ka zama Talaka me mazakuta, gara ka zama me kudi wanda bashi da maza kuta. Sanata Shehu Sani dai ya bayyana hakane a kan shafinsa na sada zumunta yayin da yake mayarwa da wani martani da yace masa ya yafi mayar da hankali kan lamarin mazakuta fiye da talaka. Lamarin ya samo Asali ne tun bayan da Sanata Shehu Sani ya wallafa magana akan matarnan data yankewa mijinta mazakuta a jihar Kaduna. Sana Sani yace "Matar da ta yankewa mijinta mazakuta a jihar Kaduna ta aikata babban laifi. Yace yawan cin zarafin mazakutar maza da ake yi ya kamata a samar da dokar da zata baiwa mazakutar maza kariya ta yanda za' daina guntuleta da zaginta da lalatata. "The woman who cuts the manhood of her husband in Kaduna has commit...
Casemiro ya saka hannun jari a kungiyar Marbella FC ta kasar Sifaniya

Casemiro ya saka hannun jari a kungiyar Marbella FC ta kasar Sifaniya

Casemiro, Labaran Manchester United
A wani abin ban mamaki, dan kwallon tsakiya na Manchester United, Casemiro ya saka hannun jari a kungiyar Marbella FC ta kasar Sifaniya. Hakanan bayan zuba hannun jarin, a yanzu ya shiga cikin daraktoci masu gudanarwa na kungiyar. Akwai dai tantamar ci gaba da zaman Casemiro a Kungiyar Manchester United indaa ake alakantashi da barin kungiyar. A ranar 3 ga watan Yuni dai an ruwaito cewa, Cristiano Ronaldo ya nemi Casemiro ya koma kungiyar Al nassr su yi wasa tare. Hakanan akwai kungiyoyin Al ahli dana Alqasidiya da suma ke zawarcin Casemiro.
Kuma dai: Kasar Israela bata daddara ba, ta sake kai harin da ya kashe sojan kasar Iran

Kuma dai: Kasar Israela bata daddara ba, ta sake kai harin da ya kashe sojan kasar Iran

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Tsaro, Yakin gaza da isra'ila
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Israela ta kai wani mummunan hari a birnin Aleppo na kasar Syria da kashe mutane da yawa ciki hadda wani sojan kasar Iran. Saidai zuwa yanzu, kasar ta Israela bata kai ga bayyana cewa itace ta kai harin ba. Wannan ne dai hari na farko tun bayan na 1 ga watan Afrilu wanda Israelan ta kai kan babban birnin Syria, Damascus wanda yayi sanadiyyar mutuwar sojojin kasar Iran. A wancan lokaci dai, kasar Iran din ta mayar da martani ta hanyar jefawa kasar Israela makamai da yawa wanda sai da kasashen Amurka, ingila da Faransa suka taru suka taresu. Wannan karin kuma ba'a san wane mataki ne kasar Iran din zata dauka akan wanan harin da Israelan ta kai mata ba.
Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Yace Ya Bada Umarnin Gyaran Dukkanin Hanyoyin Jihar Kano

Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Yace Ya Bada Umarnin Gyaran Dukkanin Hanyoyin Jihar Kano

Siyasa
Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Yace Ya Bada Umarnin Gyaran Dukkanin Hanyoyin Jihar Kano Sakamakon karatowar lokacin damuna a yanzu haka gwamnan jihar Kano ya bayar da umarni ga hukumar dake kula da titunan jihar Kano akan a tabbata duk wani titi daya samu fashewa ko zaizayewa a cikin birnin Kano a tabbatar an gyara shi domin samun nutsuwa ga masu ababen hawa. Wannan umarni da gwamnan ya bayar tuni ya fara aiki domin kuwa tuni hukumar ta KARMA ta fara aikin gyare-gyaren titunan da suka samu matsala.
Majalisar kasar Amurka ta amince da kudirin dokar da zai kakabawa kotun Duniya takunkumi saboda yunkurin ta na son kama shugaban Israela, Benjamin Netanyahu

Majalisar kasar Amurka ta amince da kudirin dokar da zai kakabawa kotun Duniya takunkumi saboda yunkurin ta na son kama shugaban Israela, Benjamin Netanyahu

Siyasa
Majalisar kasar Amurka ta amince da kudirin dokar da zai kakabawa kotun duniya takunkumi saboda hukuncin kama shugaban Israela kan kisan da yakewa Falas-dinawa. Wanda ke son a amince da wannan doka gida 247 ne sai kuma wanda basa so 155 ne wanda akan yasa kudirin ya zama doka. Dokar ta tanadi hana Visa da kuma sauran takunkumi ga duk wanda ke aiki da kotun da kuma wanda ke baiwa kotun kudin gudanarwa.
Madrid za ta tattauna da Nacho, Chelsea na zawarcin Sesko

Madrid za ta tattauna da Nacho, Chelsea na zawarcin Sesko

Wasanni
Kyaftin ɗin Real Madrid da ya lashe gasar zakarun Turai, Nacho, mai shekara 34, zai gana da ƙungiyar domin tattauna makomarsa indan kwantiragin ɗan wasan na sifaniya ya ƙare a wannan bazarar. (The Athletic) Chelsea na da ƙwarin gwiwar cewa za ta iya fafatawa da Arsenal a yunƙurin sayen ɗan wasan gaban Slovenia Benjamin Sesko mai shekara 21 daga RB Leipzig. (Standard) Arsenal na nazari kan ɗan wasan Girona da Ukraine Viktor Tsygankov, mai shekara 26, wanda AC Milan ke zawarci. (Sport) Manchester United na sha'awar sayen dan wasan bayan Everton da Ingila Jarrad Branthwaite, mai shekara 21, yayin da ta ke neman ƙarfafa ƴan wasanta na baya. Kuma tana zawarcin ɗan wasan baya na Juventus da Brazil Gleison Bremer, mai shekara 27, da ...
Hoto: An Ķàśhè Wannan Šòjan Tare Da Kwace Masa Waya A Unguwar Sarki Dake Kaduna

Hoto: An Ķàśhè Wannan Šòjan Tare Da Kwace Masa Waya A Unguwar Sarki Dake Kaduna

Tsaro
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN An Ķàśhè Wannan Šòjan Tare Da Kwace Masa Waya A Unguwar Sarki Dake Kaduna SUN YI Kl$AN KAI AKAN WAYA Wasu barayi a Unguwar Sarki Kaduna sun tare wannan Matashin ofisan Soja Lt. Isah M Abubakar akan hanyarsa na zuwa gida suka ka$he shi bayan sun kwace wayarsa Wani irin rashin imani ne wannan, a ka$he mutum saboda kawai a kwace wayarsa kuma Soja?Gaskiya akwai abin tsoro sosai game da makomarmu anan gaba Allah Ka jikansa, Ka gafarta masa, Ka karemu daga sharrin masu sharri da cutarwa.
Hukumar ‘yansanda ta saki sunayen mutane dubu 10 da suka yi nasara wajen neman aikin

Hukumar ‘yansanda ta saki sunayen mutane dubu 10 da suka yi nasara wajen neman aikin

Tsaro
Hukumar 'yansanda ta PSC ta saki bayanan mutane dubu 10 da suka yi nasarar tsallakewa mataki na gaba a neman aikin dansandan. Mutane 61,092 ne dai aka ajiye gefe wanda basu tsallake ba zuwa wannan matsayi. Hukumar tace dan tabbatar da an yi adalci wajan fitar da sunayen ta yi aiki tare da majalisar tarayya, da hukumar tabbatar da an yi raba daidai wajan bada aikin gwamnati, da kuma hukumar 'yansanda. Tace ta tabbatar an baiwa kowace karamar hukuma a Najeriya cikin 774 da ake dasu damar wakilci a cikin wadanda aka dauka din. Shugaban hukumar, Ikechukwu Ani ne ya bayyana hakan.