Saturday, March 15
Shadow

Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Kungiyar matasan Jam’iyyar SDP sun bayyana cewa basu yadda da komawar tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai Jam’iyyar ba.

Kungiyar ta bakin shugabanta, Abdulsamad Bello ta bayyana cewa, El-Rufai kawai yana son samun damar da zai cimma burinsa ne a Jam’iyyar.

Sun kara da cewa, abin takaici ne yanda Jam’iyyar ta baiwa El-Rufai dama aka tarbeshi hannu biyu-biyu ba tare da la’akarin hadarin da ke tattare dashi ba.

Matasan sun ce karamin misali shine yanda El-Rufai da ga zuwansa gashi yana son yayi kaka gida a Jam’iyyar har yayi yunkurin tsike sakataren Jam’iyyar, Dr. Olu Agunloye daga mukaminsa.

Kungiyar tace zata yaki duk wani yunkuri na neman mikawa El-Rufai Jam’iyyar inda suka gargadi shuwagabannin Jam’iyyar kada su aikata haka.

Karanta Wannan  Kallo Hotuna yanda aka gano gawar wani dan siyasa har ta fara rubewa bayan an yi gàrkùwà dashi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *