Monday, March 17
Shadow

Bamu yadda da dawowar El-Rufai Jam’iyyar mu ba, yazo ne kawai ya cimma burinsa>>Kungiyar Matasan Jam’iyyar SDP

Kungiyar matasan Jam’iyyar SDP sun bayyana cewa basu yadda da komawar tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai Jam’iyyar ba.

Kungiyar ta bakin shugabanta, Abdulsamad Bello ta bayyana cewa, El-Rufai kawai yana son samun damar da zai cimma burinsa ne a Jam’iyyar.

Sun kara da cewa, abin takaici ne yanda Jam’iyyar ta baiwa El-Rufai dama aka tarbeshi hannu biyu-biyu ba tare da la’akarin hadarin da ke tattare dashi ba.

Matasan sun ce karamin misali shine yanda El-Rufai da ga zuwansa gashi yana son yayi kaka gida a Jam’iyyar har yayi yunkurin tsike sakataren Jam’iyyar, Dr. Olu Agunloye daga mukaminsa.

Kungiyar tace zata yaki duk wani yunkuri na neman mikawa El-Rufai Jam’iyyar inda suka gargadi shuwagabannin Jam’iyyar kada su aikata haka.

Karanta Wannan  Bidiyon yanda aka kunyata wasu da aka kama suna lalata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *