
Gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara ya bayyana cewa, bai damu sai ya koma mukaminsa na gwamna ba ko ta halin kaka.
Ya bayyana hakanne a wajan wani taron tunawa da dattijon jihar, Marigayi, Edwin Clark, inda masu jawabi da yawa da auka tashi suka soki dakatar dashi da aka yi da neman a mayar dashi kujerar Gwamna.
Fubara da ya hau wajan jawabi ya nesanta kansa da kalaman mutanen inda yace bai kamata a yi fito na fito kan lamarin ba.
Ya kara da cewa, suka san ko yana son komawa Kujerar gwamnan? Yace shi a yanzu ma ruhinsa ya bar gidan Gwamnatin jihar.