Wednesday, April 29
Shadow

An dakatar da bayar da làsìsìn Màkàmì irin su Bhìndìghà ga ‘yan Najeriya dan su yi amfani da ita wajan kare kansu>>Inji Hukumar ‘yansandan Najeriya

Hukumar ‘yansandan Najeriya ta tabbatar da cewa, dokar hana bayar da lasisin Mallakar Bindiga a Najeriya dan kariyar kai har yanzu tana aiki.

Me magana da yawun hukumar, Benjamin Hundeyin ne ya bayyana haka a wani martani da yayi game da ikirarin da wani yayi cewa ya mallaki Bindigar AK47.

Benjamin yace a doka ko da ana bada lasisi, Bindigar AK47 bata cikin wadda aka amince farar hula su rike.

Yace amma a yanzu har yanzu ba’a dage dokar data hana bayar da lasisin Mallakar Bindiga dan kariyar kai ba.

Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda mutane suka rika tambayar to su tsageran daji ina suka samo nasu Bindigun?

Karanta Wannan  Yadda Mala’iku Suka Kai Ni Aljannah Har Na Gana Da Tsohon Abokina Kafin Na Dawo, Inji Godwin Ugeelu Bayan Gawarsa Ta Miƙe A Jihar Nassarawa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *